Advertisement

Ad code

kuruciyar minal 1 to 10

kuruciyar minal 1 to 10

Barka da zuwa shafinmu na littafan Hausa novels inda muka kawo muku littafin kuruciyar minal 1 to 10.

kuruciyar minal 1 to 10

CHAPTER 1

Amina ce zaune a kan wani lotsatstsen katifanta Kamar an taka bredi,basai nayi magana akan gadonta ba . Gefe wani kwano ne with a remained smelly stinky tuwo miyan kuka Wanda da alama tunna jiyane bata fitar da kwanon ba.

kuka take rizga Kamar ranta zai fita
innace ta shigo dakin domin ganin Lafiya yau yar lelenta shiru bata fito ta kama aiki ba? Turus tayi tana ganin ikon maleeku

Wani Abu na yar lele sai ita idan Ba haka Ba ya za'ayi mutum shi daya ya zauna yana kuka babu dalili.

innarce ta rafka uban salati Kamar an kama malam da karuwa tace me zangani haka aminatu Lapiya ? wa yatabo min tuwalle? me ya saki kuka?

Sai alokacin Amina ta dago ta soma magana cikin shessheka Kamar haka inna Dan Allah ki yafe min,ki roki kanwata deejeh ma tayafemin,awararta Dana karba tayi hakuri,dukan da nake mata ma na daina,kuma...kuma bazan kara zubar mata da abinci Ba kuma Wlh bazan sake kwace mata rakenta Ba Nayi alkawari har naira 50 din tama zan biyata 😭 duk rashin mutincin danakeyi Allah na dena Wlh na dena ta kara fashewa da kuka.

Galala inna tayi tana kallonta Wai yau aminatuwa ke Neman yafiya harda kiran deejeh kanwarta, lallai za'ayi ruwa da kankara
Inna tace toh yar lelen inna yi shiru kisanar dani ya akayi?me ya faru?
Minal tace inna aradu mafarki Nayi Wai cutar laser fever ta kamani Wai na mutuuu!
Inna tace kinga irinta ai mutum ace sai shegiyar kazanta yaushe Rabon da Kiyi wanka Yanzu?
Kina ganin kin kyautawa kanki kenan ?
Kuka ta fashe dashi tace kwana biyar ne kacal fa.

Inna tace ko kunyar fada bakyaji? wannan Ba laser Ba har ebola ma zata kamaki ai.
Kuka ta kara fashewa dashi tana shure-shure tace haba inna dama Ba sona kike Ba ?
Kuma ai dukda bana wanka ina canja pant fah.😭

Inna tace ni rufe wannan bakin naki karki taramun makwabta gashi duk kin cikani da warin baki.
Tashi dallah kije ki wanke baki Kiyi wanka.
Kurma ihu tayi tahau shure-shure da burbuwa.

Nan inna ta lallabata tace mata ai mafarki Ba Gaskiya bane.... haka dai ta hakura nan inna tace taje tayi wanka taci abinci Dan yau zata rubutar jarabawar karshe a makaranta daga shi next term zasuyi WAEC haka dai ta hakura ta shirya.

Ta fito zata tafi tace inna kin Tina wannan 100 Dana taba aramiki?
inna tace yaushe? tace lokacin nan sanda muka fara jarabawa
inna tace na Tina tace ki Dan banishi,inna tace haba yar inna nawa na baki atsakanin wannan lokacin?

Tuwalle tace ehheeeen wato dama badan Allah kika bani Ba inna ?!cabdi wallahi Nide sai kin bani kudin nan.

Inna tace sarkin jaraba, kin fita naci Kamar me, ta since bakin zaninta ta miko mata wata kodaddiyar Dari biyu tace ingo kuma kikawo mini canji domin shi kadaine gareni. Inna ta fadi dukda ko tasan da wuya ta kawo chanjin.
Yamutsa fuska minal tayi kamin ta karba tare da Cewa dande ina bukatar kudin ne da yasin bazan karba tsohuwar kudinnan Ba.

Nan ta rungumi inna Kamar da gaske sannan ta fita tare da Cewa sai na dawo sannan ta biya ta gidan su kawarta zaliha domin tafiya makaranta.

Koda aka tashi Tara(break) tsallaka katangan makaranta tayi taje tasiyo gurasa a kasuwa na duka kudin tayi sadaka dashi wa almajirai akan Allah ya kara rufawa iyayenta asiri

(dukda Cewa Amina akwai tsiwa da rashin mutunci ga Wanda ya nema amma akwaita da tausayin iyayenta sosai domin kazantarta Nada nasaba da haka acewarta Idan sabulu da turarenta basu Kare Ba ai iyayenta bazasu kashe kudi wajen siyan wani Ba shiyasa sau biyu take wanka a sati su inna har sun gaji da mata magana)

Amina Yusuf yarinya ce er shekara 18-19 farace sosai ga hanci shima daidai misali 8 figure ce ga tsayi daida gwargwado idonta ko sexy eyes ne gashin kanta kuwa ba'a magana.

Babanta wato malam Yusuf Wanda akafi sani da baban kowa carpenter ne bashida karfi amma yanada rufin asiri sannan duk anguwar ana ganin girmansa sosai manya da yara.

Asalin sa fulanin taraba ne wadda yarasa kowa NASA sanadiyyar gobara tun yana shekara 18 haka yarike Kansa har yakai 25 ananne ya dawo kano da zama inda ya hadu da falmata wanda ake kira da inna wacce take kanuriyar barno ce gyaran miki da turaren wuta take a kanon har sukayi aure dagabaya suka Koma Kaduna da zama Inda suke can cikin malali ahaka har inna ta haifi danta na fari wato Abubakar Wanda yanzu yake project a ABU amma shi yake rike kansa domin ya ragewa iyayenshi nauyi sannan yakanyi musu aike idan ya samu hali tunda Ba zaman banza yake Ba.

Daganan inna bata kuma haihuwa Ba sai bayan shekara takwas Inda ta Haifi Amina wacce take yarr jagwal ce ga neman magana,ga tsiwa, saide matsoraciya ce na masifa amma ta rike addininta dukda ko Ba ganewa ake Ba.

Sai daga baya inna ta Haifi khadijah wacce take auta kuma shekaranta 12.

Wannan kenan

Kubiyoni domin jin cigaban kuruciyar minal


KURUCIYAR MINAL 2

Minal rike da sakamakonta a Hannu miftahu (kanin hannatu zamu ganta a gaba #chapter 8 ) yace manya manyan Yan boko har an karbo sakamakon kenan da fatan wannan karan ma ba'a dauko ajinba. Cukumosa minal tayi ta naushi bakinsa tace aiko Ba Komai ni nane makarantar wasu a yawon banza za'a kare. Daidai lokacin sani (yayan bilkisu itama zamu gantaa gaba #chapter 8) ya wankawa minal mari juyowa tayi tace buhun bala'i bai ankareba yaga an nunashi wa sama an nana da kasa suka minal tamai jina-jina sannan tasa yara sukabuleshi da kasa.

*Evening*

A guje yara suka rugo Suna oyoyo baban kowa oyoyo baban mu! dama ya saba Dan haka yasa kullum baya rabuwa da tsaraba, hanjin ligidi mai yawa acikin bakin laida ya ciro ya basu suka karba Suna godiya kamin suka raba, wata yarinyace tace baba yau wani tatsuniya zaka mana yace tatsuniyar gizo bakin barawo zan muku.
Lado ne ya shinfida masa buhu Kamar yadda suka saba sannan Suma yaran suka zazzauna nan dattijonnan ya soma musu ta tsuniya......

🌹.............

Wasu samarine zaune Suna busa sigari wayan dayansu ta soma kara daukowa yayi yaga karfe alarm dinsa na large hudu ne take ya kashe sigarinsa yace kai yau fa alarm NASA mana aradu lokacin dawowan tsohonnan yayi,dariya suka fashe dashi wani yace Ba mamaki ya tsaya yiwa yara tatsuniyane. Sukace Ba shakka amma fa tsohonnan yana yiwa mutane cikas ka duba abinda yar b*ra ub*an yarnan tasa tayi dazu.
Daidai lokacin baban kowa ya karyo kwana,a take suka karkade jikinsu tare da wulla alewa a baki Dan kar yaji warin sigarin tasu.

Nufosa suka farayi Kamar abin arziki shima da murmushinsa yaje nufosu domin yaune karo nafarko dabai kamasu Suna busa sigari Ba.

Saide kash suna motsowa kusa dashi ya jiyota aiko take annurin fuskarsa ta dauke sukace babanmu sannu da zuwa Suna masu durkusawa

bata rai yayi yace Duba su Kamar da haske Kamar mutanen arziki, Wai Ku fi sabillilahi bazakuyi wa kanku fada ba, Kamar da gaske nadau kunyi hankali Ashe da sauran Rina a kaba,

Bakusan cewa wannan shaye shayen naku yana janyowa iyayenku Bacin sunaba?ko kunaso duniya tazagesu ne?girgiza kai sukayi sukace ayi hakuri baban mu Insha Allah zamu daina.

murmushi takaici yayi domin Indai wannan alkawarinne to an karyasa tun kafin adaukesa yace Allah ya bada ikon dainawan,kuna batawa kanku rayuwa ko bakusan Cewa duk abinda mutum yayi yana kuruciyar shi zai bishi har girma ba ko kunaso idan kun hayayyafa acewa yaranku kun taba busa wiwi ?girgiza kai sukayi yace Idan yaranku suka sha Ku ya zakuji hada baki sukayi wajen Cewa bazamuji dadi ba yace Idan Baku sani bama Ku sani wannan shaye shayen yana haifar da tabin hankalin,lalacewar koda da zuciya kuma tsaf zai kashe mutum. Ku a haka zaku hadu da Allah? Kuma kuna tunanin Idan an tafi a haka ba matsala?Ba Arabic Ba bokon?Allah ya Shirya....

Tafiyarsa ya cigaba dayi yana mai fada akan yadda matasa ke bata rayuwarsu.

Majalisar su malam yakubu zai wuce sukace salamu alaikum baban kowa barka da war haka murmushi ya soma musu sannan ya mika musu hannu sukayi musabaha.
Malam isa mai wankin hula ne yace ya naganka haka ne ? baban kowa yace kaide bari yaran yanzu basu rabuwa da kayan bakin ciki yanzu na.....

Malam saminu ne yazo yana girgiza kai alamun alajabi jikinsa a sanyaye ya zauna
Baban kowa yace haba malam saminu ya haka zakazo ka zauna bako sallama? inkai kayi haka 'yan'yan mu kuma yaya zasuyi ?

Malam saminu ne ya cire hularsa ya ajiye kana yace wato wani abune yayi mugun jijjigani, Wai yar gidan malam ado salma akayiwa fyade saboda sakacin maihaifiyarta. fita tayi bayan magariba ba'a saniba uwar kuma da bata ganta Ba bata nemeta Ba sai da taga kusan goma ya wuce shine ta Sanar da malam adon. neman duniya an mata ba'a ganta Ba yau da asuba aka yadda ita koda aka kaita asubiti likitoci nata kokarinsu amma ina. yanxu yanzunnan rai yayi halinsa,Allah ya mata rasuwa!

Shiru wajen ya dauka kamin caaan malam sambo Wanda tun dazu baiyi magana ba yace Wai salma dai guda Dana sani yar shekara 6?itafa wannan salmar dai inji malam saminu
Salati suka rafka jikin kowa yayi mugun sanyi kamar an musu duka.
Allah sarki salma yarinya mai hankali da Shiga rai. Allah yaji kanta bari anjima sai mu hadu muje muyi masa ta'aziya nan dai suka Dan tad'a kamin malam Yusuf yayi gidansa.

Koda yake tafiya a hanya sai surfo masa gaisuwa ake ta ko'ina manya da yara. Atakaice de baban kowa mai jama'a ne.

Yana isowa kofar gidan sa, basheer mai shago yace baban kowa ina wuni,Lpy klau basheeru ya shagon?basheer yace Alhamdullah baban kowa yace masha dafatan dai yauma minal bata taba kowa Ba Dan yau da safe tace Mani Wai tun jiya akace suje su karbo sakamakonsu. Basheer yace Gaskiya baban kowa yau minal bata yi hayaniya da kowa Ba hasalima ko fitowanta bangani wadda nima abin ya bani mamaki da alamu dai kawattamu ta natsu(haka basheer din ke kiranta domin ya kasance abokin ya abubakar ne tun yarinta shiyasa ma yayiwa baban kowan karya Dan kar yasa wa ransa damuwa sosai)
Baban kowa yace to Masha Allah haka akeso ai ni bara in Shiga Daga ciki ko? Allah yayi albarka basheer yace amin.

Minal na zaune tana yanka kubewa taji sallamar mahaifinta hantar cikinta ne ya kada da gudu ta mike har tana tuntube a 360 ta fada daki,garin sauri ta barar da yakuwar da take yankawa innace ta haba er lele lafiyarki kuwa zaki barar mani da......

Bata ida maganar ba baban kowa ya shigo yana cewa inata sallamma Baku amsa ba Kamar ba kowa a gidan inna tace yi hakuri malam sannu da dawowa Wlh wannan yarinyarnance ta fada daki da gudu har tayi Mani bari banjika ba yi hakuri bara na kawo ma ruwa
Takalmin sa ya cire ya zauna a tabarmar dake shinfide a tsakar gidan yana Cewa halan wayanta aka kira take wannan gudu , inna dake shirin bude randa domin sachet watern su ya kare tace anya kuwa?hira fa muke daga jin sallamarka ta rusa da gudu Kamar taga aljani,baban kowa najin haka jikin sa yayi sanyi bayason irin faduwsrnan da yarda keyi a makaranta domin Hanson tayi karatu ta inganta rayuwarta

Yace takarbo sakamakon jarabawar tasu kuwa inna tace eh ta karbo dazu gasucan yana kan yana kan taaga(window),tashi yayi jiki babu kwari ya dauko ya Duba aiko Kamar yadda yace ne ankuma na 48 tazo acikin su 52 a Dan fusace yaje kofar dakin yace aminatu me kikeyi acikin dakin nan,minal tace Riga make canjawa yace inba so kike na Shiga Ba maza ki fito tace baba aradu Babu Riga ajikina wanka make shirin yi yace Kamar da haske rabon da Kiyi wanka keda kanji Ba tare da dance Kiyi Ba yanzu shekaru 6 kenan amma shikenan ni bara in dubo sakona waje.

Oya show some love
By voting,
liking,
sharing
and
commenting

Tnxs for reading


KURUCIYAR MINAL 3

Sanda ta kara kusan 5min sannan ta leko da kanta duk ta hada gumi saboda rashin gaskiya

Saukan rankwashin da tajine yasa ta sankare a wurin na wani sakanni.

Durkushewa tayi a wurin tana tutturo baki kamar zai taba kofa.
Baba ne yace rufi min baki kamin in kara miki,maza tashi.

Mikewa yayi tana zuzzunburewa tace haba baba ko Dan wannan rankwashin da kake samani kamar abinci Ba dole na KASA kokari Ba kana taba min CPU na bakasan Cewa itace masarrafin Dan Adam ba?

yace yimin shiru kamin in da'da maki wani yar kaniya kawai,me kwakwalwar kifi Allah dai ya bude maki wannan toshesshiyar kwakwalwar taki.

kuka ta fara yi tana buga kafa ni Gaskiya baba kwakwalwata ba a toshetake baaa inna tace ni yimin shiru karki taramin makwabta ehe.

Murya ta kara baba yace bari kiga ikon Allah mikewa yayi ya dauko sanda.
yanda Kasan Anyi ruwan sama an dauke tsit ta shanye kukan da takeyi tana tsitstsilla idanu tare da sheshsheka baba yace banson jin sheshekar nan. Ki natsu bari inga tsiyar da kika shukowa mutane wannan karan.

Mutum bashida aiki sai fada ni Nayi mamaki ma yau kusan sati 2 ba'a kawo kararki Ba.
Turo baki tayi duk yasha mai sai yalki take tace yo ai dannayi mafarkin na mutu ne kuma ko yanxu ma Ba fasawa nayi Ba.

Kallonta baba yake har ta ida maganan ta already ya Ciro takalmi Dan haka ya lafta mata.

papers din ya fara dubawa yaga  subjects 2 ne takeda A amma saura Wai sai a slow saide rubutun nan war inka gani zaka dauka wata Dr ce tayishi sai ka karantawane kaji Kamar kayi kuka.

takaicin rashin kokari na diyartasa abar kaunarsa ne ya taso mai.

Kansa  kawai yake girgizawa saboda takaici bazai musaba Idan akace masa Dan primary five ma yafi yar tasa kokari.

Tsawa ya daka mata ke zonan !
Simi simi taje ya kalleta sannan yace yanxu ke ahakan zaki tafi makarantar gaba?ki Duba fa gododuwar banza da wofi. Murmushi tayi
inna tace Allah zanci mutuncinki ana miki fada kina dariya saboda kin daina mutane ko? Tace Toh Toh Toh ni inna me Nayi ? Dakuwa inna ta mata tace kaniyarki kikayi

tace to yi hakuri bazan kara Ba shikenan aiko?yauwa inata Dan Allah ki siyan awara?harara inna ta banks mata tace ba'a siya dinba
Baba dake jinsu  ya tattare takardun yana cewa ace mutum anmai repeat har sau biyu amma bai gyara ba nasan duk ajin keda zaliha kun fisu girma amma kanku Kamar kifi har gara ita akanke.
antara dakikai biyu a aji daya bakuda aiki sai ciye ciye kuma da kunada kokarinku tunda kuka fara Hulda da wannan fatiman shikenan lamuranku ya tabarbare.

tace toh Ba kai kake Bani kuddin Ba? Kuma ai fatimamma sun Koma kano.

Yace au haka zakice?

Inna tace kaga malam rabu da ita kar hawan jininka ya tashi
Mika ma innatakardun yayi yace jeki ajiye min adakin ki Dan in ina ganinsu takaici ne zai kasheni

ni inanan ina fafitikar biya miki WAEC kan arufe amma naga alama asara zanyi

Zama kusa dashi tayi ta Washe baki tace baba kawai ka barni in fara aiki a gidan abinci Dan Gaskiya ni karatun bokonnan sai a hakali bazan maka karya in batama lokaci da dukiya ba yasin dakyar in zan hada ko credit 4 me kyau a wannan WAYES din
Yasin Gaskiya kake fadi kwakwalwartawa a to she take nakifinne maganarka Ba karya.

Abin yaso bashi dariya amma sai ya Girgiza kai

yace ai ga irintanan ana WAEC kina WAYES dubaki ko ajikinki Yan ajinku zasu makarantar gaba amma ke oho ko ?kinacewa inbarki Kiyi aiki a gidan abinci

Bakiji abinda ya faru da salma Ba ko 'yar gidan malam ado ?tana gidan ubanta ma ba'abarta Ba balleke budurwa kin tallata kanki a gidan abinci
Nan ya labarta musu abinda ya samu salma sannan yace Suma suje suyi ta'aziya.
Inna kam salati take harda kwalla tace kai duniyar nan Ba imani.

Minal ko mikewa tayi tana bubbuga kafa tace Toni baba idan ma bazaka iya barina inyo aikin Ba kawai kamin aure ka huta
Ai da gudu sukayo kanta ba shiri tayi waje tare da Jan mayafi akan igiya.
Baba yace da shegiyar kazanta ma wa zai soki?ja'ira yar kwal uba
Inna tace abita da addu'a da fata na gari kawai.

🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀

Wakarta takeyi tana tafiya ta hango murtala da wani abokinsa mai kawo masa ziyara babba yake kowa?waishi a dole Santa yaje. Zukar sigari suke Suna busa abarsu.

Tsayuwa tayi a wajensu tace anya murtala kanada hankali kuwa kullum kayita busawa 'ya'yan hanjin ka hayaki Kana biyewa wannan sha katafin?

Dariya ya bushe dashi kamin yace minal kenan ai na Fiki  hankali ma. Babba yace ke yar shila karki kawao mana raini Anan fa ko kinga sa'anki ananne?

Bata kulashiba taci gaba da yiwa murtala magana da tayi:
Dalla tafi can wallahi baka isa ba kayi kadan.

Kaikuma ta nuna babba da yarda kama daina nuna ka sanniwata kila ma sanadinka ne samari basa kulani to ka kiyaye ni.

Babba ne ya bushe da dariya Hahaha sannan yace kinfaiyi kwantai babu mai sonki sai yawo a unguwa

Dariyar takaici ta kyalkyale dashi kamin tace kaji banza botorami, yo da na Sauri miji irinka a gara na zauna Ba aure sha katafi kawai. Kuma in mijin agidan uban mutum ake rabawa sai ya hanani.
Murtala yace Ke yarinyannan zanyi maganinki fa, abokin bawa kuke fadawa maganar banza?

Minal tace da wacce itaciyar zakayi magani na? Kasan ni annobace da banida magani. Nan gani nan bari dumamen mayya in fada ma.

Murtala yace  kinci darajar babanki mutumin kirki ne kuma banason rigima yau da kinga yadda ake balla kafar yarinya. Tace yo inba tsoro Ba kamaso mana wallahi kaga yadda na fito dinnan babu mutunci.... Mtsw ni banma da lokacin Dan shaye.

Tafiya tayi abunta,babba Wanda ya tsaya yana kallonta sai alokacin yace kai murtala babe dinnan tayi aradu. Kaga jiki me kyau kuwa........

Tsaki murtala yaja kamin ya tashi yabar wajen yana gunaguni akan irin yadda babban ya nuna halin ko in kula gameda abinda minal din tamai.

KURUCIYAR MINAL 4


*UNGUWAN SARKI,KADUNA STATE.*

Unguwa ne hadadde da manya manyan mutanen Nigeria masu matsayi da kudi ke zama,unguwa ne na wadanda sukakai a dama dasu.
Wani mansion ne dankararre Wanda yaji kayan alatu na duniya

Wasu mutane ne ke zagaye da gidan sanye da uniform daga ganinsu kuratan sojoji ne irin masu gadin gidajen oganninsu nan gaban gidan faranni ne of different colours and nature sunyi das das dasu sun kawata gidan
Wani katafaren gate nagani black with a touch of golden ta gefe naga an rubuta JEEDMAR on golden plate

The house has single side but classified into 3 which contain 12 fully furnitured bedrooms
with bathrooms in each containing fully jaccuzis and all other necessary things,3 parlours with cotton softened chairs,beautifully decorated dining room with a 10 people dining table,mordern kitchen,fully equipt gym room,sports field,3 swimming pools of different shape,size and designs,fully flowered and fruited garden,office dinshi,car parks with the most latest and expensive cars parked in,securities' side,workers'(helpers') side.

Motoci ne guda 11 suka shigo gidan sunyi convoy dukan su bakake ne banda na tsakiya Wanda yake fari wani kurtun sojane yazo ya bude motar
Wani kyakkyawa,dogo,fari,mai saje,ga diri tabarakallah masha Allah Kamar balarabe ne naga ya fito sanya yake cikin kayan sojoji fuskannan a daure babu alamun wasa ko kadan dukka sojojinne suka Sara masa a tare baiko kulasu Ba ya shige ciki abinsa.

Mahaifiyarsa ya Tarar zaune a parlour tana kallon news ga fruit a gefe tanasha hankali kwance cikin fara'a da walwalan ganin mahaifiyarsa abin kaunar sa yace mom! jin muryan Rabin ranta kuma danta wato CPT YAZEED ABDULMAJEED UMAR ta tashi yazo da sauri ya rungumeta tare da manna mata peck a kumatu yana fadin I missed u mom itama tace missed you too son

Dama tun dazu shi take jira domin tasan da dawowarsa
Tace son go and fresh up sai kazo kaci abinci ko smiling yayi yace okay mom tare da hayewa middle staircase coz shine nashi the one left for his wife zakiyya and the one on right for his mom.

Bathroom ya fada direct Ba tare da tinanin Komai Ba ya cika jacuzzi da ruwa yasa bathing soap and perfume ya shiga ciki ya rufe idonsa tinanin zakiyya ne ya fado mai,
shikam ya rasa yadda zaiyi da itA sai kace Ba auren soyayya sukayi Ba ace Sam batada time dinshi yauma da zai dawo daga tafiya she can't stay at home just for a day thank goodness he hasn't let her become a full-working wife as she wanted or else Hhhhhhh iska ya furzar domin abin ya fara isanshi Gaskiya saboda ko hakkinshi na aure yanxu da kyar yake karba agurinta.

Ganin tinananin bazai fisheshi Ba yasa ya gama wanka ya daura alwala, da Rigan wanka zai sa ya Fasa ya daura towel ya fito rike da karami yana goge silky,soft and dark hair dinshi he looking so sexy (Kamar yadda naji Yan mata na fadi danni haryau wannan shirmen baya birgeni amma danku sai na rubuta ko ya kukace? You are my first priority.)

CPT YAZEED ABDULMAJEED UMAR kenan! a 35years old son of late ALH. ABDULMAJEED UMAR

ALHAJI ABDULMAJEED UMAR is a multi millionaire international businessman with the organisations and companies namely jeedmar empire, jeedmar furnitures,jeedmar shoes and clothing,jeedmar oil company, jeedmar rice,jeedmar sugar,jeedmar cement,jeedmar orphanage and much more.
Asalinsa fulanin zamfara bayan ya gama karatu ya fara business ikon Allah cikin kankanin lokaci ya bunkasa har ya fara companies a different countries a yawon kasuwancinsa ne ya hadu da mom wacce take Nigerian-arabian wato babanta Dan Nigeria mamarta er riyad(saudi)amma a Dubai suke zaune.
Sun hadune ta sanadiyyar babanta saboda Suna kasuwanci tare sannan ya gaba da hankalinshi.
Haka dai sukayi aure kuma lokaci daya soyayya mai karfi ya Shiga tsakaninsu amma Abu daya suka rasa haihuwa haka sukayi shekara 12 Ba ko batan wata tukunna daga baya Allah ya dube su da idon rahama ya basu da namiji wadda suka samai YAZEED tun yana Yaro yakeson armies shi baya kallon cartoon irin na yara in ka Ganshi ya na kallo to sojoji ne har faint na dakin shi na sojoji ne. wata rana ALHAJI ABDULMAJEED ya tattari family dinshi gaba daya akan zasuje aikin hajji dukda Cewa wasu daga cikinsu sun sha zuwa amma wannan karon a tare yakeso suje saide mom bataje Ba itada YAZEED domin Ba tada Lpy sai akabarta tare da kakus Maman ALHAJI ABDULMAJEED.

Bayan sun sauke farali ahanyarsu ta dawowa sukayi hatsari a jirgi inda yawanci suka rarrasu wasu kuma suka sami matsalan haihuwa shi kuma ALHAJI ABDULMAJEED was paralysed. Alokacin YAZEED na shekara 13 saboda tsananin Sabon da yayi da mahaifinsa hakan yasa ya zama so moody rayuwarsa duk ta canja ya zama shiru shiru lokacin dayatafi makarantar sojoji at that tym he was 25 Anan aka aiko masa da rasuwar mahaifinsa yayi kuka har ya gaji tun daga lokacin aka dena gane kansa bayan ya kammala ya dawo anane ya saida some companies na dad dinshi to the some Arabian and British partners na dad din nasa wasu kuma ya rarrabawa family members marasa karfi sosai akan su kular mai da companies din,sai su dinga yin 50 50 atakaice de bai rike ko company daya Ba domin shi soja yakeson zama.

Alokacin da yaje wani mission a Washington Anan ne ya hadu da zaliha lokacin tana shekararta na karshe a university wasa wasa soyayya maikarfi ya Shiga tsakaninsu bayan ta kammala sukayi aure amma ita tace burinta aduniya shine ta zama businesswoman amma YAZEED yace shi bazai iya juran zama babu mace a kusa dashi Ba amma idan ta yarda zai bude mata boutique
Ganin da babu gara ba dadi yasa ta yarda plaza guda ya siya ya mayar mata boutique da office dinta aciki Dana wasu masu mukamai kadan daga cikin masu aikinta.
Amma duk da haka bai tsira Ba domin kullum batada aiki sai boutique da ka tabata boutique dinta kawai ko lokacin kanta batada shi.

Wannan kenan

Show some love by
Sharing,
And
Commenting.

KURUCIYAR MINAL 5

Bayan ganin tunani bazai fisheshi Ba yasa ya shafa mai ya saka 3quater irin na sojoji da farin T-shirt ya fito mahaifiyarsa ya Tatar a parlourn tace son sai yanxu?Sosa kai yayi yace sorry mom dina na I kept you waiting ko?

Tace is okay,come and eat your food coz na sanka idan ta kai ne zaka wuni bakaci abinci Ba gashi nan yanzu ulcer ta maka kamin kawo wuka

Yace haba mom ya isa mana zanci muje dining din haka ta kama hannunshi takaishi taja masa kujera ya zauna ta zuba mai abincin yace kai mom this is too much tace see you, wannan abincin a 5 years old child can eat it but you hmm you will never change
smiling kawai yayi yafara ci.

Baifi 6 spoons yayi bah yace ya koshi babu yadda mom batayi Ba yace Sam ya koshi haka ta rabu dashi yaje daki domin ya huta

11:59pm (night)

Suna zaune a parlour yana kan cinyarta tana shafa gashinsa Suna Dan hirar su na uwa da d'a zakiyya ce ta shigo taci wani suit na mata takalminnan dogo Kamar zai karye
kwas kwas kwas kakejin takun takalmin ta koda ta shigo ta gansu kawai hannun tadanyi using irin hii dinnan kamin tace wlcm baby tawuce abinta

Girgiza kai kawai mom tayi kamin ta juyo ta lura Cewa dan nata na matukar son yabi matarsa amma kunyan idonta yakeji hakan yasa tace kai dagani ka gani bacci nakeji Ba musu ya tashi tare da mata peck yace good night mom sannan yahau stair case din dazai Sada shi da side din da matarshi take.

ZAKIYYA'S POV

Tana shiga dakinta ta yarda jakanta ta fara cire takalminta kamin ta fara rage kayan jikinta tare da daukan ribbon tana kokarin daure Malaysian attached wig dake kanta Wanda yake red,blue and black in colour taji anyi hugging dinta ta baya

Tsaki tayi kamin tace look baby am soo tired,and am not in d mood so leave me alone pls shinshinan wuyanta ya farayi yana Cewa I missed you Bea tasan sarai me yae nufi hakan yasa tayi saurin tureshi tare da fadawa toilet.

Koda ta fito yana zaune a kan gado Kamar maye yana jiranta bata ko kalli Inda yake Ba taje ta daura hannunta akan wani Dan machine Wanda zaiyi detecting tomb print dinta Wardrobe dinta ne ya baiyyana yayi typing nighties sai daya daga cikin kofofin Wardrobe din suka bude ta dauka wani brown din nylon riga tasa iya guiwa tazo ta kwannta tare da Cewa switch off d light when you are done taja bargo tare da juyamai baya

Mamaki ne ya cikashi Wai dama batasonshi ne ta aureshi koko wani abinne ya sameta coz wata matace za'ace mijinta yayi tafiya ya dawo babu ko sannu da zuwan arziki balle ayi zancen su abinci. Duk da Cewa ya saba da irin halinnan NATA amma nayau is worse haka dai yayi ta sake sake daga karshe yaje ya kwanta a bayanta yana Dan tattabata bige hannunsa tayi yace baby pls Wallahi I need you kinji ?
yadda yayi maganar ya bata tausayi hakan yasa tarabu dashi amma sai mita take masa Wai tagaji hakan yasa bai sami wani biyan bukata sosaiba masu iya magana na cewa da babu gwara Ba dadi

Koda ya tashi da asuba ya tasheta he entered the toilet did all the necessary routine,came out and found her still sleeping ya sake tashinta sannan ya fita masallati ta koma ta kwanta abinta har sai 6 ta tashi Wai bazata iyayin sallahn Ba sai ta dawo(ehm araina nace inkin dawo kuma kice kin gaji Ba Allah sai ya kyauta).

Around 7 ya dawo direct dakinshi ya wuce ya kwanta itako lokacin harta shirya tasaka pink suit mai wandon pelazu ta sauko sai shan kamshi take, ta buga uban extension akai sai yarfeshi take
Mom ce zaune a falo tana kallon news ayayinda take shan coffee,hade rai tayi domin bataso ganin mom din a parlourn ba.

Tace good morning mom,mom tace morning
Zata wuce mom tace zonan zakiyya
Zuwa tayi ta tsaya tana Duba agogonta
Mom tace yanxu abinda kikeyi ya dace kenan ki Duba wani shigar yahudawa da kikeyi koni Balarabiya banyiba,kuma ki fita tun safe sai dare sannan baki ko girmama mijinki balle ni ai ko............
Bata karashe Ba zakiyya tace sorry mom inaso boutique dina ya tsaya dakafarsa sosaine kamin in Dan dinga samun time yanxu fai Ba wa'azi nakeso Ba ince de matsalarki bana girkine to me kikeso kici?ta fadi hakan cikin Sauri tana Duba agogonta domin tayi latti acewarta.

Mom ta girgiza kai tace zakiyya kenan so nake naci koko da kosai tace okay kitchen ta Shiga tabi wata kofa Wanda zai sada ta side din ma'aikata taje bangaren masu girki tace pop out
Cikin kankanin lokaci sukayi layi a gabanta sanda tagama zuba musu kallon raini sannan tace waya iya koko da kosai duk sukayi shiru domin Continental dish yawanci suka iya
tsawa ta daka musu Ba daku nakeba ?

Emm kwanna biyu ban tsokalo muku minal ba karkudamu yanxu Muka soma tafiya

KURUCIYAR MINAL 6

Daya daga cikinsu ne tace na taba gani kakata tayi may be zan iya
Zakiyya tace oya do it right away and take it to that old shit watace tafito faga toilet tana bada hakuri kan Lattin da tayi wani wawan mari ta sauke mata tare da Cewa you are fired hakuri ta fara bata tana Cewa cikinta ne ya baci ta kewaya amma ko kallonta batayi Ba

Tanashigowa parlourn tace mom am off,mom tace haba zakiyya wannan kayan naki Kamar Ba musulma Ba zaki fita dasu kije ki saka mayafi mana

Bata rai tayi tana zunbure zunbure da huhhura hanci taje tasako wani Dan karamin hijabi

Tana fita ta tubeshi tare da Cewa haka kawai duk abi a takurawa mutum mtsww

Zaune take a office tana wani business deal
Telephone ta dauka ta dannan wasu lambobi bugu daya ya shiga tace coffee sannan ta kashe wata ce ta shigo dauke da kofin shayi ta ajiye tajuya tana tafiya kenan taji ruwan coffee a bayanta wani tsalle ta daka tare da Cewa jesus! Heeee I don finish oooo chai my back,my back

Zaliha ce ta wanka mata mari tare da Cewa keep your mouth shut,
Tsit tayi amma idonta bai dena zubda hawaye Ba

Are you out of your sense ya zaki kawomin coffee with white sugar while you knew that Brown sugar nakesha
Sorry ma I was not d one dat prepared the tea it was Sade.
Are you crazy?was is it not your job to make my tea? why will Sade do it?Jennifer!you are fired
Cikin kuka tace ma am sorry

Sakina is absent so I am the one attending to the customers that's why am sorry ma

Shiru tayi kamin ta juya taje ta zauna tace I will give you last chance but if you make any mistake in the future sorry for yourself
Common get out of my office

Tashi tayi tana thank you ma,Tnx u kamin ta fita

Abangaren mom kuwa Anyi mata wani busheshshen kosai da wani tsulan kunu me gudaje kawai kallon abincin ta tsaya tanayi aranta tana Cewa"ya zama dole in nemo wadda ta iya abincin gargajiya Dan ni shekaru na ya fara ja I can't always cook for my self la astadi'u wallah"

YAZEED kuwa sanda ya tashi duk ya gaji addu'an tashi daya bacci yayi Kamar haka (alhamdulillahil lazi ahyaniy ba'ada ma amataniy wa ilaihin nushuur )sannan ya sauka daga king size bed dinshi ya Shiga toilet yayi all the necessary routine sannan yayi wanka ya fito ya Shirya cikin kanan kaya

Yazeed's bedroom

�?

sannan ya fita domin yin break fast koda ya fito mom ya tarar tasa wani jagwalgwalo a gabanta domin shi baisan me kosai bama balle wannan kosan dayayi baki Kamar za'a bawa akuya

Morning mom ya fada ganin bata kulashi Ba yasa ya fahimci Cewa tunani take

Dafata yayi kamin yace mom wats wrong firgit tayi tace son had ka tashi morning
Yace morning amma tinanin me kikeyi mom tace bakomai kawai ina tunanin karo mai aiki ne Wanda she will only cook and take care of me coz duk wannan masu aikin are modern ni kuma na fara tsufa am 54 fa danma inada jiki mai kyau wani sai ya dauka am 50 so dole na rage wasu abubuwan danake yi da kaina especially abinci na
yace to mom how do u expect us to find one

Tace assign one of your soldiers to go to any restaurant that cooks traditional food and then look for the best cook inso samune mace coz banson namiji yana yawo acikin gida

Okay I will try nande akabar wannan kosan kaddaran sukaje dining table tasha tea abinta shiko chips egg and plantain yaci
Sai brown coffee coz bai fiya shan black one Ba.
Bayan sun gama cin abincin side dinshi ya nufa yaje master balcony yana tunani rayuwarsa da zakiyya

Abangaren minal kuwa direct gidan su zaliha ta nufa bayan ta gama da Yan unguwantasu. Shiganta kenan iya(Maman zaliha) tace wa nake gani anan Kamar aminatu 'yar jagwal?yau Anyi abin kai sai yanxu aka shigo? Ai mutumiyartaki tana tanata tsumayinki.

Bata rai tayi tace haba iya ni Gaskiya ki dena ce Mani yar jagwal to me zance aminatu aike da kinzo guri sai kin kawo matsala da kinzo Guri ake sanin kinzo gashi kullum sai kinzo gidan yar tsohuwa tafadi hakan cikin tsokana.

Kara bata rai tayi kamin ta tace wannan kanki ni ina zally take

Iya tace yaran zamani da wani shekiyanci suke yanzu zalihan ne ya koma zalla Toh tana daki ai sai ki Shiga

Shiga tayi ta sameta tana bacci daka mata duka tayi a gadon baya tace shegiya baccin asara ko? ana la'asar kina bacci

Zaliha tashi tayi harda er tusarta tana zare ido Dan atunaninta iya ne domin ta hanata baccin la'asar
Tsaki ta buga lokacin da taga minal ce

Ke Wai me hakan mutun na bacci kin wani daka masa duka

Amina tace tsabar rashin Gaskiya kuma harda tusa ba
Suka fashe da dariya

Haka suka cigaba da hira kamin suka tashi sukayi sallan la'asar suka Shirya domin tafiya makaranta

Ahanyansu na tafiya ne zaliha ke Cewa minal gobe zata rakata gurin aunty fauziyya(auntyn zaliha ne wato Kanwar mahaifinta yaranta uku Aisha ,Abubakar da Muhammad tana Sana'an snacks)
Abubakar ya karye jiya a makaranta
minal tace dama Yaro da shegen kiriniya Ba dole ya karye idan Baku hanashi Ba gaba gaba har wasu zaina karyawa

Zaliha tace garashi yarone

Minal tace to me kike nufi tace me ko nake nufi?
Tace babu fa ta bude baki zatayi magane ta hango wasu en mata en Iskan anguwansu an caba ado za'aje yawon bariki Suna ganinta suka fara bata rai domin haushinta sukeji Wai ta fisu kyau,domin ko Kamar inna ta dauko amma hasken baba dukda Cewa innan ma Ba baka bace amma batada haske sosai amma akwai gashi masha Allah Wanda amina har tafita hakama kyau

Suna zuwa zasu wuce daya daga cikinsu mai Suna bilkisu(bakace er lukuta mai katon timbi ga katon lebe da boobs yadda kasan kwarya saide batada hips Wanda hakan yasa ta zama Kamar an ajiye buhun hatsi gata gajeruwa anci red lipstick,brows dinnan ba'a magana) ta bangaji Amina da kafada

Dan cika amina ta cika amma sai ta basar saboda tunda tayi mafarkin laser fever ya kasheta ta rage jagwal

Ganin bata kulasu Ba yasa sameera (doguwace siriiiiriya gashi batada shape,Ba gaba Ba baya atakaice de yadda Kasan sandar snooker ko ince 1 irinsu akewa kirarin singul amama no front no back gashi taci uwar bleaching had tafara zama danyen nama),
Tace ke Amina wannan wani irin iskanci ne zaki mangari billy ko hakuri bazaki bata ba

Amina batace Komai Ba ta ci gaba da tafiya
hannatu ce(wannan ita ba'a magana)tazo ta bankade Amina.
Ai ji kake tas! tas!! tas!!!

To readers wa aka wanka wa mari haka Indai Amina aka Mara to Ba zaman lapiya

Nide bara in labe daga bayan bishiya in debo muku rahoto

Give me some bossa !

By
Voting
Sharing
Commenting
And
Liking

Your er uwa mai nishadan tarwa da fadakarwa

KURUCIYAR MINAL 7

Wani wawan mari amina ta sakewa hannatu har sanda taga tauraro
Sameera ce ta hayaiyako zata daki amina,wani lafiyaiyan mari
Amina ta aika mata atake ta dauke wuta ta suma zaliha ce tace ni amina zo mutafi kamin kisa da naushi Kiyi kisa taja hannunta suka tafi ayayinda akabar bilkisu sakoko a tsaye batada tudun dafawa gashi yau zasu wanki wani alhaji yace su ukun za'a hada lokaci daya (Allah shi kyauta)

Atake taji wani bakin ciki ya rufeta taji ta kara tsanan amina.....

Amina kuwa dasuka je islamiyya sunyi latti gashi malam isa ke taran latti ya iya bulala Kamar Allah ne ya aiko shi

Shikadai ne yake iya dealing da amina kuma tana tsoransa sosai amma tsabar bakin ciki da haushin daya rufe mata ido bata lura dashi Ba
Sai saukar bulala da taji batasan sanda ta karbi bulalan ta karya Ba hade da banka masa harara ayayinda ta murkuda cute pinky lips dinta tace Allah ya isa ta wuce

Malam isa sai da yasha jinin jikinsa domin yasan yadda take tsoranshi(saboda ya iya bulala itakuma duk abinda zai taba lafiyar jikinta bataso)
amma yau harda karya bulala wadda take tsoro Kamar maciji gashi fiskanta yayi jaaa(red)alamun Bacin rai kuma dama shima dai yana shakkunta karfin hali ne kawai irin nasa amma ya girgiza yau Dan haka satinnan dole ya Dan tsagaitawa amina idan Ba hakaba shima zai karbi rabonsa ko ta kullo masa jagwal.
Haka suka Shiga aji Amina tasha mur,zaliha nata aikin ban hakuri hakadai har aka tashi suka dawo gida tana kumbure kumbure.

Bayan sallan magriba inna ta gama abinci ta kwalawa Amina kira bata amsa Ba ta kara kwala mata kira still shiru abinda bata tabayi Ba kenan akirata taki amsawa shiga dakin inna tayi thinking that something is wrong with her daughter to her surprise Amina was sitting down on her mattress

Ke er lele dama kina jina kikai shiru to abincin ki zaki dauka she didn't reply inna rather all she did was sip water from her tiny blue cup

Inna tace er nan Ba lafiya Dan a yadda nasanki ko bata maki rai akayi baki wasa da tuwo amma yau ko motsi bakiyi
Ta fadi hakanne ayayinda take taba goshin Amina Dan inna ji take Amina batada Lpy domin ita bata wasa da tuwo

Jin ko magana batayiba yasa inna ta fita ta samu baba ta labarta masa abinda ta gani baba ne yace rabu da ita zamu hadu atakaice de ranan Amina bataci abinci ba.

Washe gari koda Amina ta tashi tayi shara da wanke wanke ta gama koko,
Sai wajen karfe goma ta tuna da Cewa zata raka zahra anguwa tashi tayi tasa hijabi taje dakin inna tace inna ni zan tafi gidansu zahra tace zan rakata anguwa

wani kallo inna ta watsa mata kamin tace shine gaisuwan ki ?

Amina tace mantawa Nayi ina kwana
Inna tace rike abinki
Sannan a haka zaki rakata anguwan kai Innalillahi aminatu yaushe zaki canza yau kwana uku kenan bakiyi wanka kuma a haka kike tunanin zaki samu miji ki Duba kullum in zahra zatazo gidannan kwas da ita amma ke a birkice

Since bakin zaninta tayi ta miko mata Dari biyu ki siyo sabulu da tirare dan d'uri da sabulun gashi kinji

Bubbuga kafa Amina ta fara haba inna zan bata mata lokaci fa
inna tace to wallahi inbakiyi abinda na fada Ba babu Inda zaki mutum sai shegen kazanta Allah ma daya taimaka bakida karnin kashi ai da mun mutu

Turo baki tayi tana guna guni har ta siyo ta dawo
Inna tace maza Shiga wanka ki wanke kanki sai kizo in miki kitso saura kiyimin gardama ma babu inda zaki
Subul subul tayi Kamar yadda inna ta umarceta ta shiga ban dakin shiru shiru babu ita babu labarinta inna tace wai me kike yine har yanzu kinsan dai jiranki nakeyi ko?

Fitowa tayi gefen kanta duk kunfa inna tace ke haka ake wankar duk dadewannan nanki baki daurayu Ba? Bata ko kula innar Ba ta shigewarta daki ta goge kan sosai ya zama saura damshi sannan ta zauna aka mata kitson ta dauko kayanta mai Dan haske ta saka sannan ta Dan shafa man baki sai tayi dass da ita.

Tana fitowa inna tace ko kefa amma ace mutum bayason wanka minal tace inna kwana biyu ne fa inna tace kaji banziya ko kunya bakiji har kina daga murya gararin makota suji

Tace to Nide na tafi tana fitowa Zaure ta hadu da baba tace baba ina kwana yace Lpy a'a aminatu ce haka ko bake bafa amma ace mutum kullum...............

Tace to baba ya isa mana tunda Nayi wankan yace yauwa er gari kinga in kina Dan kwalliyan nanne zaki samu miji ko Ba haka ba
murmushi tayi ya miko mata naira Dari yace na sanki da awara watakilla shi zakije siyowa ko innan ki ce ta aike ki
tace a'a gidan su zaliha zani zan rakata anguwa Dan auntyn ta ya karye kuma zamu tayata gyaran gida dashi ke basu Dade da kaura wannan gidan Ba
Baba yace Toh sai kin dawo amma karkiyi dare tace Toh kamin ta fita tanayi masa godiyan kudin daya bata

Tana fita tace Kamar baba yasan banda kudi wlh

Abangaren YAZEED kuwa yau ana shiri da mitimiyar domin bataje office Ba,
Ya Shirya musu evening outing zaliha anci ado makeup kamar ya zubo daga fiskanta attachment dinnan ba'a magana sai harhada rai take wai ita adole batason raini(nace uhm shi baice zaki rainashiba sai ke?)

Taku daidai take har ta iso gaban wani Mercedes Benz sai yauki take alokacin YAZEED ya Dade yana jiranta domin yace shi da kanshi zai tuka su kuma bayason escort na soldiers ko daya.

How is the novel?is it good?any suggestions?

Ramadan Mubarak and happy sallah in advance

KURUCIYAR MINAL 8

Tana shigowa ya kunna mota domin yaji haushin bata masa time da tayi domin he values time so much. Tafiya suke a hankali babu Wanda ya kula kowa

🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹

Abangaren minal kuwa ta isa gidan su zally ta sameta tana kwalliya an rike mirror da bakin eye pencil sai zana girannan ake baki wuluk abin abin dariya

'Daka mata duka tayi a cinya
Kinga abinda kika jawomin ko? kullum in zakije anguwa saboda iyayi sai kinyi kwalliya kinsa inna ta Mani kitson dole ta sani kwalliya.

Sai alokacin zally ta kalle ta tace kawai kice kinyi kwalliya kinaso ki nuna mini  shine zaki fake da guzuma ki harbi karsana!
To wallahi bashi dukannan.

Minal tace wannan ke ta shafa sannan ta zauna tace kinsan yau Dana hadu da baba a Zaure na dauka duka na zaiyi saboda tabarar danayi musu a gidan

Ga mamaki na bemin maganar Ba kuma harda bani kudi
zally tace iye lallai kwalliya ta biya kudin sabulu,wato haduwar taki har akan baba tayi tasiri, yo ina batun su babba?hararanta minal tayi taci gaba da cewa amma matsalata dake ko kwalliyan baki iya Ba kinsan mu yan boko kuma wayayyu anaso adinga yin make up mai kyau amma kin wani shafa powder da man baki

Minal tace iye sannu wayaiya yar boko.
Zaliha tace ke nifa zan cigaba da karatu domin suleiman yanason inyi karatu har kudin WAEC ya biya min a wata makarantar private kuma yace zai Nayi mini lesson in munyi aure.

Minal tace lallai ma yarinyarnan wato haka zamuyi dake? tafiya makarantar gaba zakiyi ki barni?

Zaliha tace a ah zama zanyi in jiraki harsai kin zama farfesiya

kallon zaliha minal takeyi yayinda zalihar taci gaba da kwalliyarta.

Can zaliha tace ni yanzu banida burin daya wuce in Tara kudin Indan siya man kara haske Dan ba'kina yayi yawa wallahi.

Minal tace man me?! Sauri zaliha tayi ta rufe mata baki tace toh sannu sarkin karadi so kike iya taji ko?

Tureta minal tayi tace to in tajin ma ai haka akeso ni ban taba Sanin bakida hankali bama sai yau,ke bakisan Cewa butulci wa Allah bane ace yayi ki baka kice Wai bakinki yayi yawa ? Kin FISA sanin daidai ne? Kuma ai koba Komai mayukan blitin dinnan yana 'bata fata bara kij,i kuma iyada lahani sosai saima kinji ciwo in yaki warkewa zakiyi bayani.
Karkiga ke baka ce wallahi wani zai iya mutuwa akan bakar mace kuma wallahi sai kiga fara ko a kafa aka daura masa sai ya kunceta.
Kima godewa Allah kinada kyau farare nawa ne munana?mtswww!

Ajiyan zuciya zaliha ta sauke kamin tace kuma fa maganar ki Gaskiya ne waje daya kika kwafsa Ba man blitin akace Ba bleaching ake Cewa. minal tace Koma menene Nide tashi mu tafi.

Zaliha tace Gaskiya kizo na Dan miki kwalliya minal tace Wanda Nayi ma ya isa.

Tace shiyasa bazaki taba samun saurayi Ba ki Duba ki gani kafin a tsaida lokacin aurena samarina dayawa

Amma ke wa ya taba miki kallon birgewa ma

Shiru minal tayi kamin tace kuma fa hakane wato shine sirrin baki taba fadamin Bako,Allah ya isa

Zaliha tace ai shiyasa kullum inna ke miki fada akan wanka baki gane Ba

Minal tace to me mike jira zana mini ado Yan mata

zama tayi zaliha ta shafa mata Jan powder aka zana girannan akayi mata Layin baki da green

Yadda Kasan er tashe

Fitowa sukayi zasu tafi sukayiwa iya sallama tanata kodasu Wai en matanta zasu haska titi

Koda suka fita zaliha ta ballawa Amina harara tace er uwa matsalata dake baza'a taba iya gyaraki Ba kaf duniya Ba Wanda zai iya in aka gyara nan sai asamo wani matsalan

wannan wani irin tafiyane?
Minal tace me matsalar tafiyannawa ?

zally tace kinga yanda ake tafiya yanga ta soma Kamar talotalo (lol karfa kuce ina kushe characters dina zasu Waye, just for entertainment ne 😂😂)

Minal ma ta fara kwaikwayanta abin har gwara na Zally domin minal ita nata Kamar agwagwa😂.

Ana cikin haka aka fara ruwa Kamar da bakin kwarya
Yan matanka suka nemi wurin buya domin kada ruwa ya musu duka,

amma sanda aka sami matsala domin ya ca'be musu ado

Abangaren yazeed kuwa parking yayi domin ruwan ya tsagaita ganin zakky baby ta 'bata masa lokaci gashi ko kulashi batayi Ba balle yasa ran zata bashi hakuri abin sai ya bata masa rai

Yace
Zakky what's all of this ?

Tace
Meaning?

Yace
first you wasted my time,also came out walking like a snail and you can't even apologize?

Tace
What wrong have I done that I will apologise? Is it wrong to walk majestically?
Look that's fashion

She said that Prolonging the fashion

Yace
Fashion my foot,the hell with it

Alokacin ruwan ya tsaya kunna motan yayi
Ayayinda zakky ke Cewa

Look idan ka fito dani just to disgrace me ne am not in the mood please hurry up ma ni am starving gushhh

Wani wawan acceleration ya kwasa ya kure speed din motan shi dama ba mutane akan titin

Alokacin dadai su zaliha sun fito daga Inda suka labe domin su tsallaka titi takalmin minal ya Tsinke tsallakawa zaliha tayi koda ta juya ta hango minal bata tsallako Ba tace Ki tsallako kamin abawa motocin Hannu .

Minal tace ke aradu sai na gyara takalmi na.
Zaliha tace wallahi ko ki tsallako ko in tafi in tafiyata minal tace da nace ki jiranine?
Tsugunawa tayi ta cire takalmin ta fara kokarin gyarawa yayinda zaliha tayi tafiyatta tana mai jin haushin minal din.

Neman kara minal ta farayi bata zamu Ba aiko tana Daga kanta taga wani a tsakiyar titi Dan haka Ba tare da nazari Ba ta hay kan titin domin burinta kawai ta gara takalmin ta.

Alokacin kuwa aka bada Hannu kuma daidai lokacin fada ya kaure tsakanin zakiyya da yazeed CeCe kuce suke tayi yana hankalinsa kenan daga titi yana Cewa zakky don't try me this evening

Minal kuwa ta dauko karanta tana kokarin gyara takalmin tare da tafiya a hankali akan titin domin itama ta tsallaka taga mota a guje yana iyowa kanta
Duk kayan cikinta sanda suka kada.

Daidai lokacin yazeed ya lura da ita kokarin kaucewa yayi ya fada cikin wani Dan rami Wanda ruwa ya taru kuma ya daki motan wani

Tun daga sama har kasa yawatsawa minal ruwa ta sule ta fadi kasa yayinda mai dayan motan ya fito......................

Hahhhh finally

This is my sallah gift to u guys hope you like this chapter

NOTE:
All pictures of characters shown here are not related to the story.

Kindly share, and comment thank you

Much love

4th June 2019

KURUCIYAR MINAL 9

Juyowa yazeed yayi ya kalli zakiyya yace oh gush,look at the mess you cause!

Minal ko lokacin da ta d'aga idonta taga Wanda ya watsa mata ruwa ya juya yana magana da wata(saboda motar Ba ita yake using ba babu tinted)abin ya mugu bata haushi

Minal ta fara magana a hankali lallai ma mutuminnan ya watsa mini ruwa sannan ya tsaya magana da budurwarsa?

Mikewa tayi zata zazzaga masa rashin mutunci daidai lokacin me motan nan ya fito yazeed dake shirin fitowa shima yace bawan Allah kayi hakuri....

Mutumin ne yayi saurin katseshi ta hanyar Cewa  wa make gaji Kamar captain yazeed murmushi yazeed yayi yace nine Dan Allah a Duba ma asarar da Nayi sai inbiya ga card dina ya fadi hakan yana kokarin bawa katinsa mutumin yace ka barshi kawai yallabai ai paint nema ya Dan kurje Gaskiya Muna alfari dakai a ka sannan Allah ya kara yi maka jagora yazeed yace ameen amma dan Allah ko wannan ne ka karba mutumin yace waneni ranka shi Dade kuda kuka bamu rayuwarku Dan kukaremu shine har sai na karbi kudinka Dan ka gurjemin mota?ai kake wallahi Ba Komai sai alolacin ya lura da zakiyya cikin fara'a yace ina wuni madam ? Ya tsine tayi kamin kasa kasa tace lafiya tana mai kauda kai.
Dariya mutuminne ya dauke yace ranka shi Dade zamu iya yin selfie? Murmushi yazeed yayi yace Ba matsala. Quick selfie mutumin ya musu sannan ya Shiga motarsa yana mamakin abinda zakiyya tamai dukda ko bai Santa Ba amma da alamu tanada alaja da yazeed din.

Yazeed ko da ya mance da ya watsawa minal ruwa dukda ko laifinta ne tana tafiya ahankali akan titi amma shima harda laifinsa daya biyewa zakiyya ya kunna motarsa zai wuce minal tayi saurin riko hannun kofar

sauke glass yace baiwar Allah dan Allah Kiyi hakuri ban lura bane wallahi hankalina ne ya sauke Daga titin amma kema hada laifinki kina tsallaka titi bakya kallo ki kula Dan Allah

ya fadi haka yayinda ya zabgawa zakiyya harara yana kokarin Ciro kudin a aljihunsa.

ganin zakiyya ta fashe da dariya, abin ya kara bawa minal haushi

Su watsa mata ruwa amma ko su kallo Inda take yarda wani tsayawa Suna surutu da photo da wani mutumi sai kace Yan film bayan sun gama Iskancin nasu zasu ta fita rikosu shine ya wani kwame a mota yana bata hakuri
Sannan budurwarsa tana mata dariya

kwafa minal tayi kamin ta kama kwankwaso ta fara jijjiga tayi kicin kicin da ido

Tace wallahi Allah ya isa na ya za'ayi Ku watsan ruwa kuma kunai mini dariya

Babu abinda yazeed ya tsana Kamar ayi masa Allah ya isa
Hakan yasa shi mugun mamaki amma ganin fiskanta kwalliyar ta cabe bakinnan sai yalki yake Kamar tasha man gyada

Abin ya basa dariya amma ya shanye,50k ya miko mata yace gashi ki siya sabulu  kije a Duba ki kiji kanwata ?

Minal tace me kuddin zai min kuma babu wani batun Kanwarka ni karkayi min zakin baki Dan bazaiyi aiki Anan Ba. Ta fadi hakan sannan ta murkutsa baki

The girl is now getting on his nerves

He just pressed his car accelerator trying to leave

Not yet Mr.yazeed abdulmajeed

Wani tsalle minal ta daka ta sake rike hannun kofarsa

Zakiyya babu abinda take sai dariya Dan ita ganin clown takeyiwa minal,fadan nasu yana kayatar da ita hakan yasa ta dauko wayarta ta fara video.

Malam ya zaka watsamin ruwa ka kusa bigeni har na fadi kasa amma ka hakimce a mota kana miko mini kudi me zanyi da kudinka?ai fitowa zakayi ka Duba Lpy ta.

Fitowa yayi a harzuke

Kusa da ita yazo ta daga kanta

Wai Wai Wai wannan dakyar in takai kafadansa ma tabdi

Ai bata lura gardi bane wannan sai sai basamude ma ai da batayi masa rashin kunya ba.