Advertisement

Ad code

AUREN YARJEJENIYA 3

AUREN YARJEJENIYA 3

AUREN YARJEJENIYA 3: wani had'add'en garden ne na hutawa wanda da kaga wajen zaka tabbatar da if you're not in the first social class baza kazo wajen ba"ko ina Akwai grass carpet"zaune take gaban wani table"hand bag nata da wayarta na A Ajiye samqn table d'in"tayi shiru ta lula Aduniyar tunani"Iska na marecen yau laraba na kad'awa gwanin dad'i....gefen zuciyarta kuma tana jiran isowar k'awarta lawisa Awajen"kasancewar tana son zuwa nan wajen dan yana mugun d'ebe mata kewa"tana sanye da jallabiya bak'a ta yane kanta da mayafin"bak'in gashin dake gaban goshinta ya bayyana"babu make up a samqn farar fuskarta Amma haka be hana kyawunta bayyanaba" dan tanada kyau kamar Aljannah"kimanin kwana 4 kenan dataga wani guy Anan dg nesa"saidai har yanzun zuciyarta ta kasa mantashi da manta fuskarsa"dukda tanada wanda zata Aura nanda shekara d'aya da rabi"koshi batajinsa Aranta kamar yadda takeji dataga wannan guy d'in"d'ago kanta tayi sbd motsin mutane dataji"kowa nata harkan gabansa"wasu samari da y'an matan nata fira suna shan drinks ko ice cream"wasu kuma manyan mutanene suna maganar data shafi Aikinsu.......

Gabanta yayi mugun bugawa! sbd hango guy d'in datayi dg gaba yana tafiya" sai mutane wasu Abayansa wasu Agefensa suna biye dashi"kallo d'aya ta musu ta d'auke kanta......jama'a pls ku d'an koma d'aga can ciki sbd big man ya iso"kuma nan farko farko yafi yawan zama shida muta nansa"cewar wasu security's dake Aiki Anan"sosai Abin yabama *ummul khairy* mamaki"kud'i ta biya ta shigo wajen da sauran mutane"haka shima kud'i ya biya to Akan me za'a ce su matsa ?wayafi Anan wajen??"dukta tambayi kanta Acikin zuciyarta"batare data san wama Ake nufi da big man d'in ba"juyowa tayi da mamaki taga duk gaban tables d'in bbu mutane sun koma can gaba"sai ita kad'ai kawai....tj yaja tsaki yana fad'in ita waccan meyasa barata tashi ba bayan Ansanar kowa ya matsa??junuid yace"sbd tana tak'amar k'ilan tanada kyau ko?sam Abdallah be lura da ummul khairy dake zaune ba can nesa"saida yaji kalaman su tj sannan ya lura da ita"kamal yabisu da kallo sbd yafahimci suna k'ok'arin d'ora big man hanyar banza yadinga wulak'anta mutane"wanda shima jiya Aka bashi sallama yabiyosu nan d'ansu d'ebe kewa"kallo d'aya big man yamata yaji wani irin mugun haushinta"musammun daya lura ko Ajikinta tanama danna waya ma"bayan Ansanar kowa yatashi sbd raini shine ta zauna ga sa'an wasanta ko??"duk ya Ayyanah hakan Aransa yana cije baki"yana nufar table d'in da ummu ke zaune"wanda tun kafin ya iso k'amshin turarensa ya rigasa isowa"su tj na biye dashi"gaban ummu yafad'i data fahimci nan suka doso"saidai ta had'e rai sbd itama bata d'aukar raini"tana kuma tambayar kanta idan sun iso miye zasuyi mata to??"........

Cike da izzah da gadara Abdallah dake sanye da k'ananun kayan da suka masa masifar kyau yatsaya daga gefenta yanata cin magani"kamal ya kalleta ya kallesa"bbu wanda yayi mgn"cikin zazzak'ar muryarta tace"malamai bashi ko tara konaci ban biyaba da zakuzo kumin tsaye samqn kai??"ta fad'a cikin masifa"tj yace"ke dallah rufema mutane baki"kinsan gaban kowa kike ne?"ko kuwa bakiji Ance kutashi Anan ba big man ke zama nan waje Jen da mutanansa...ummu bata ko kalli gefen da tj yake ba"sbd lokaci guda taji wata muguwar tsanarsa"Abdallah ta kallah suka had'a ido"Atare k'irjinsu ya buga!"dukda yamata kwarjini taji kuma mugun shakkarsa Arabta Amma batajin zata iya nunawa"harara me rai da lafiya ta wurgo masa tana fad'in malam lafiya zaka tasani gaba kana kallo??"tukunnah ma waye shi wanda wannan d'an koron ke zuzutawa haka?"inaso na gansa naji yanada wuta ko aljannah balle yasakani ciki??"kud'i na biya na shigo nan kuma sune kuka biya kuka shigo ko?to Akan me zan tashi sbd wani?"bbu wanda ya isa yakafamun doka Anan"ta k'are maganar cikin k'arfin hali da nuna ko Ajikinta"kamal yasaki murmushi sbd yaji yarinyar tayi bala'in burgesa data disga TJ tanuna kuma bata tsoron kowa"Abdallah ya kallah yaga bbu Alamar rahama Asaman kyakykyawar fuskarsa"yana dai bin ummu da wani irin mugun kallo.....ke !dakata karki gaya mamu maganar banza"ga big man nan Agabanki"zai iya b'atar dake da Ahalinki bbu Abinda zai ita faruwa"zakizo kina gayama mutane mgn son ranki"ko Anfad'a miki kinada Ajin dazai kulaki ne??"cewar junuid"kamal yace"pls ya isa haka"duk kace nace be tasoba"ta fad'i iya gaskiyarta ne"yaka mata muje ga kujeru can mu zauna dan banga Amfanin tsayuwarmu Anan ba"wani banzan kallo junuid da tj sukabi kamal dashi"yayinda ummu gabanta keta dukan tara tara "ranta yabata wannan kyakykyawan mutumin shine big man"tayi mamakin izzarsa da har yanzun beyi mgn ba yana dai tsaye yana danna waya"yayinda Acikin zuciyarta taji kamal ya burgeta sbd gaskiyar dayake fad'a"tana wannan tunanin ta d'auki hand bag nata da wayarta ta mik'e tsaye da nufin tabar musu wajen"saidai tanaso ta wuce shi kuma yana tsaye bbu dama dole saiya gyara sannan ta wuce"kamal kuwa yayi mamakin Abdallah sbd yasan be shiga sabgar mata"saidai ranshi yabashi kodai cin mutunci zaiyiwa yarinyar nan"wacce yaga Alamar tarbiyya da kamun kai Atare da ita"musammun dayaga bata damu ko rikicewa da ganin big man ba.....ka gyara zan wuce! sanyayyar muryar ummu ta katsema kamal tunaninsa"Abdallah ya d'auki kusan second 10 kafin ya d'ago kansa ya watsa mata manyan idanuwansa"Atake taji k'irjinta yabuga"ta d'aure fuska tana d'auke kanta"koma matsowa yayi dab da ita har tana jin hucin numfashin sa"subahanallahi! ta fad'a tana matsawa"K wawiya! yafad'a cikin daka tsawa"hakan be hana tattausan muryanshi bayyanah ba"kin isa ki tsaya ki gayamun mgn ki kuma wanye lafiya??"never idan kinyi wannan tunanin"yafad'a yana girgiza kansa yanuna ta da yatsa"dubeki shashasha jiki na d'oyi da tsami"Ayanzun zan nuna miki tabbas inada k'arfin iko"banida wuta banida Aljannah Amma zakisan inada k'arfin iko ga wanda yyi gigin shiga gonata"


KARANTA: AUREN YARJEJENIYA 4