Advertisement

Ad code

Tame Gari Complete Hausa Novel

 

Tame Gari Complete Hausa Novel

Tame Gari Complete Hausa Novel

Ta me Gari NA khadija usman

BISMILLAHIR RAHMANIRRAHIM

1

Na rantse da Allah bazan yadda ba sai an biyani nikana tun

kin isa ma wlh kika sake kika je kika fadawa innata yaseen sai kinci ubanki cewar dije dake kara tattake garin dake zube a kasa kuma an barar din duk ranar da kika qara cemin dijan gala tame gari tuwon gidanku ma zanje in barar wlh

su Shatu dake gefe suna kallo ba damar suyi magana dije taci uwarsu dan haka sukayi gum ko yi hakurin sun kasa fada hafsi kuwa sai rizgar kukanta takeyi dan tasan yau idan taje gida kashinta ya bushe gurin delu dan saita mata dukan mutuwa kuma tasata nemo mata wani garin koda ta tuna ai saita kara bare baki dije ce ta kalleta tace wai ke uwar me nayi miki da kiketa min wannan kukan danma ban faffasa miki baki ba hegiya me idon gyada

shatu ce ta karaso kusa da ita tace kin san delu dukanta zatayi idan taje gida kin san dai ba imani ne da ita ba

shuru dije tayi na dan wani lokaci kamar wadda ta tuna wani abun sannan kuma tace toh kinga ke kika jawo wa kanki tunda kika tsoka ne ni amma kiyi haquri kinji tahi nasan yadda zamuyi amma sai kin bani hakuri

da sauri hafsi tace yi haquri dan Allah

toh naji ya sunana

Anti dije

wani farin ciki ne ya mamaye zuciyarta dan tana masifar son sunan nan na 'yan binni dan haka da sauri tacewa hafsi taso muje gidanmu in baki dawar ki kara kaiwa nikan

da sauri hafsi ta mike dan tasan ko yanzu takai nikan sai ta ci ubanta dan ta jima dan haka da sauri suka je gidansu dije koda suka je dije bata boyewa inna saudi komai ba aikuwa ta basu dawa suka kai nika har gida dije suka raka hafsi aikuwa delu kamar ta ari baki taita jarabar ta dayake 'yan dukan basa kusa sun dai samu rabon zagi amma bata daki hafsi ba

********
mota ce kirar honda Accord LC ta shigo cikin garin Gawo kasancewar rashin kyawun hanyar ga kuma da alama wanda ke cikin motar yasha tafiya mutum biyu ne ciki matasan samari kyawawa daka gansu kaga wadanda hutu da nera suka zauna a wajen tuki yakeyi kamar wanda aka yiwa dole kafin ya waiga ya kalli dayan yace cikin kasalalliyar muryarsa

Habeeb wlh nagaji dayawa na matsu mu qarasa cikin garin nan in yada zango kan gadon tsohon nan

wanda aka kira da habeeb yayi murmushi kafin yace hmm kaima kenan bare kuma ni dana sha tafiya kwana nan gashi yau ma son ganin wannan me ran karfen yasa na biyoka

hmmm kai dai bari ai wannan tsohon inaga rokon Allah yakeyi mana shiyasa bama iya daukar lokaci bamu ganshi ba ko daddy ma fa kullum shi batun shi baba malam kusan koyaushe yana kan hanya

toh Allah yaja da kwana dai

Ameen ya Allah

kam bala'i ta fada yayin da taga motar na kokarin shigewa alamar ma na ciki besan me yayi ba giginyar dake hannunta ta dauka ta saita glass din motar ta wurga cikin sa'a kuwa ta daki glass din side driver sannan taje ta hada da bakin habeeb wanda yagama amsawa da ameen yanzu

wani wawan birki ya taka tare da kiran ya Allah sbd ganin abun da yayi kamar a mafarki dubansa yakai inda habeeb yake yaga nan da nan bakinsa ya haye ya wani kumbura kamar bakin jaba ga kuma jini na zuba yaso yayi dariya harga Allah amma ba hali dole ya ambaci kalmar subahanallah ya fara kokarin bude motar ya fito danya zagaya gurin habeeb dan shi har yanzu baisan ta inda abin yafaru ba amma dai kawai yaga wulgawar abu

tsaye take ta rike kugu da hannu daya dayan kuma wata katuwar giginyar ce datafi ta farko girma
kwalliyar fuskarta kawai yagani yaji gabansa ya fadi dan wlh babu tantama wannan aljana ce

wa'innahu sulaimanu wa'innahu bismillahir rahmanir raheem ya fara ambata cike da tsoro da faduwar gaba domin dai babu tantama wannan aljana ce duba da yanayin ta gata fara sol saika ce zabiya ga kuma uban bakin kwalli data shafa a bakin nan kamar 'yar auta ga jagira cinku ta hade da kwallin dataja hawayen masoyi

jikinsa ne ya hau kyarma inda ita kuma dije take ta fahimci meyake nufi aikuwa a zuciyarta tace anzo gurin

harara taci gaba da wurga masa tanata juya ido inda shikuma hakan ke kara firgita shi cikin karkarwar jiki ya qarasa inda habeeb yake ya sunkuyar da kansa kasa sakamakon nauyin daya yi masa sbd giginyar ta bugi kansa ga haqorinsa guda daya daya fita ga bakin ya kumbura yayi tsayi kamar shantu cikin rawar jiki Nasir yakarasa inda yake ya bude murfin motar yana me karanta duk addu'ar data zo bakinsa dago kansa yayi ya dubeshi jin yanata kwarara addu'a sai ya fahimci lallai gamo sukayi domin ya hango aljanar tsaye da irin tasu giginyar ta Aljanu tanata juya ido duk da jirin dayake ji hakan bai hanashi rudewa ba shima ya kama kokarin fitowar nan suka kankame juna shida nasir wanda har kwalla yafara yi dan tsoro musamman duba da yayi da yanayin gurin babu komai sai tarin bishiyoyi da besan kona meye ba amma dai yasan harda na kuka kuma sune gidan aljanu

cikin wata irin murya da malkwada harshe dije tace ku bil adama daga ina

wani irin fitsari ne ya kufcewa naseer shiko habeeb ji yayi kamar ya suma dan kanshi saida ya amsa

ko bakwa ji ne ina tambayarku?

cikin in i na nasir yace yi....yi..ha.k..uri.daga Abuja Abuja wlh muka zo

shine aka ce dan kunzo daga binni kubi takan 'ya'yana suna tsaka da yin wasan su wato sbd kun raina mu ko

ah ah wlh ba...bahaka bane wlh ku kuke ganinmu bamu muke ganinku ba dan girman Allah kiyi haquri wlh bamu sani ba

toh naji zan hakura amma sai dai kubar abin hawanku anan ku qarasa da kafarku inda zaku ko kuma ni inkai ku

ah ah wlh mun gode suka fada a tare zamu karasa da kafarmu ina ke ina wahala akanmu

hahahahahaha
tayi dariya sannan tace saini dije uwar aljanu ku wuce amma fa bazan kyaleku ba duba da yadda kuka raunata 'ya'yana yanzu haka suna bangon duniya wajen me magani dan haka sai naje naga yadda jikinsu yake tukunna kafin in san wanne hukunci zanyi muku

kuuuuu cikin nasir yayi wata kara dan girman Allah kiyi hakuri wlh bamu san dasu bane ina mu ina aikata haka muna sane

toh naji ku tashi ku tafi gobe kuzo ku dauke wannan motar amma ba yau ba

to toh toh mun yadda wlh

sam habeeb yakasa tafiya yayin da naseer ne ya kamashi da kyar yasaba a kafada ya miki hanya bako waiwaye harda hadawa da dan gudu bako waiwaye

tunda dije taga haka  ta zube a gurin tanata dariya harda hawaye a irin wannan yanayin su shatu suka qaraso suka risketa nan suka shiga tambayarta sam kin fada musu tayi gashi ba damar su matsa ta dankari banza dan karfi ne da ita kamar yaki inji su duk ta fisu karfi

sai da tayi me isarta kafin ta mike tace mu tafi

hafsi ce tayi karfin halin tambayarta ina gyadar da kika samo ?

ban sani ba tafada tana harararta

ai kuwa tayi gum suka ci gaba dactafiya da zarara ta tuno yadda bakin habeeb ya koma da kuma yadda taga Naseer yayi fitsari saita kuma kyalkyalewa da dariya sudai su hafsi nasu ido amma ba damar tambaya sai uwar gayyar ta so bada labari dakanta

*****
tafiya yakeyi ya hada zufa ga habeeb na cikin wani hali da taimakon Allah da taimakon wasu matasa daya sansu a gidan baba malam suka qarasa da shi gida


*TA ME GARI*

2

*ina neman afuwarku sakamakon jina shuru da kukayi a littafina ZARGI NE SILA Insha Allahu shima zan karasa muku shi nan kusa uzuri ne yasha kaina*

  ba karamin tashin hankali baba malam ya shiga ba ganin halin dasu habeeb suka shigo cikin rudewa ya shiga tambayarsu lfy ko hadari sukayi

sam naseer baya cikin nutsuwarsa abinda kawai yake iya fada shine gamo mukayi malam aljana wlh aljana ce

subahanallah!!!

malam ya fada kafin ya ce aje a kirawo muntari me chemist don ya duba habeeb domin yaga yana jin jiki da alama

bayan an gama masa duk abinda yakamata ayi masa harda allura malam kuwa rubutu yayi musu tare da tofa musu addu'oi sbd dukansu sun firgice daga baya suka samu bacci su duka kowa yanata al'ajabin abun wai aljana toh ko a ina suka ganta oho

****

da wakarta ta shigo tana rerawa inda ko sallama batayi ba ta shigo innah dake zaune tana dama fura tace kai kai dije nidai naga ranar da zakiyi hankali wlh ace da girmanki amma kina abu kamar wata karamar yarinya ni wai makarantar Allan ma anya idan na turaki kina zuwa kuwa ?

turo baki tayi gaba sannan tace ina zuwa mana toh ba'a can na iya karatun sallah ba kuma dai bari in fada miki tsakani da Allah ina zuwa in labe wani lokacin bayan ajin su mairo ta gidan me gari in ta kallonsu ana koya musu karatun arna

haba inna saudi ta rike tace oh ni saude nagamu da ja'irar yarinya wato duk hanaki din danayi wato baki jiba ko saida kika dinga zuwa Allah ya shirye ki

Ameen dan kuwa yanzu ma a shirye nake kamar carbi

kasa magana inna tayi a ranta tana jinjina kiriniya irinta dije tarasa dalili ko dan taga ita kadai ce ohoo haka dai taci gaba da damun furarta ita ko dije ta shiga cikin daki ta kwanta a cewarta saitayi bacci kuma kada a tasheta tana kwanciya ta tuna da abinda yafaru dazu aikuwa ta sheke da dariya wadda saida inna ta taso ta lekata taganta sai dariya takeyi harda rike ciki girgiza kai kawai tayi ta saki labulen dan ita lamarin dije sai addu,a wani lokacin idan tayi abu kamar me aljanu

*Asalin labarin*

Malam muhammadu
dan asalin jigawa ne yanada mata hudu da tarin yara matarsa ta fari nada yara shidda maza ta biyu kuwa yaranta tara bakawai mata biyu maza ta ukun nada yara biyu duk maza sai Amaryarsa dake da yara goma sha daya tara maxa biyu mata Alhmdlh gidan akwai zaman lfy da hadin kai domin ya gina gidansa da zaman lfy dazumunci mariya itace matarsa ta uku itace keda yara biyu inusa da Auwalu duk cikin matan sa tafi hakuri da kawaici hakan yasa yaranta suma sukayi sanyun hali irin nata sam basu da hayanikuma dukansu manoma ne sosai yayin da dukansu sukai aure kuma barakallah dukansu suna nan da rai malam inusa nada mata daya wato saude Allah be azurtasu da haihuwa ba tsawon lokaci sai daga baya suka fara samu amma kuma yaran wabi sukeyi saida tayi haihuwa hudu haka kafin daga baya tasamu cikin dijee cikin hukuncin Allah kuma ita ta rayu khadija ta taso yarinya kyakkyawa fara ce sol irin fararen nan ne sosai sai dai fa batajin magana duk wata tsokana da caskale ta kware akai dan haka yara sa'anninta ke tsoronta inda har suka samata suna bata sani ba wato uwar mazga

a cikin 'ya'yan malam muhammadu dayawa daga cikinsu sun sami cigaban rayuwa inda sukayi karatun boko wasu sun sami aiki a birni wasu kuwa kasuwanci yakaisu kuma cikin ikon Allah ansami daukaka da wadata inda malam muhammadu yake da matansa suke samun kulawa a yanzu haka shine matsayin me gari wanda su habeeb 'ya'ya ne ga dansa babba wato khamis dake aiki a abuja sam basu dade da dawowa daga U.S ba inda suka shafe shekara goma sha biyu a can dan a can sukayi karatun su na secondry har zuwa jami'a indadukan su suka karanci fannin likiktanci shi habeeh ganygoicial shi kuma Naseer consultant ne yanzu haka satinsu biyu da dawowa shine suketa zaga dangi dan suna son kauye basu da kyama sam

*cigaban labari*

uwar mazga nata sharar bacci cikin baccin ma mafarkin su habeeb tayita yi wai har da zawo naseer yayi aikuwa take ta qara rushewa da dariya wadda ta qara jawo hankalin inna ganin da tayi tanata bacci ba ruwanta yasata tashinta dan itafa ta gama gasgata aljanu ne da dije

*****
inna saudi ce ta fito dauke da kwarya cike da fura inda dije dake zaune gefen babanta yana cin tuwo tanata zuba mishi surutu inna saudi tace malam na fito bari inyi sauri inje in dawo inga jikin nasu dije taso muje ki rakani dan dare ne yanzu yafi mu tafi mu biyu

ah ah ni ba inda zani ai munyi fada da baba malam shiyasa jiya da hafsi tace min dijangala tame gari na barar mata da gari ni yanzu nayi yaji saiya zo biko

dariya sukayi dukansu inda malam inusa yace yi tafiyarki kinji kyale wannan uwar rigimar

ai bama saika ce ba ni nayi gaba saina dawo

a dawo lfy innata

Allah yasa

tasa kai ta fice

gyara zamanta tayi tace baba wai ni waye beda lfy ne a gidan me gari ?

yayyenki ne na abuja wai gamo sukayi da aljana a hanyar su ta shigowa gar......ai be qarasa ba yaga ta mike ta suri takalma tana bari inje in raka inna sai na dawo ta zura da gudu tabarsshi da sakin baki kafin daga baya yayi murmushi yace Allah ya shiryamin ke dije ta

****
bata riski inna a hanya ba dan ba hanyar datayi tsammani tabi ba kusan a tare suka isa amma innah sam bata ganta ba ta shige gidan bayan sun gaisa da surikanta ta shiga bangaren mai gari ta gaisheshi tare da su habeeb wadanda suka warware amma kumburin bakin habeeb na nan idan nasir ya kalle shi saiya qara fashewa da dariya iya kuluwa habeeb ya kulu jiyakeyi inda ba aljana bace tayi musu haka ba wlh da mutum ne bema san me zaiyi masa ba a haka inna ta musu sallama tana dada jajanta abin kafin ta miqe tayi musu sallama ta fita

a kofar gida ta riski me gari zaune bisa kujerar sa ta tsoffi ta lababa ta shige gidan indayana kallonta amma ya qyaleta dan yasan halin mutuniyar tunda bataso kulashi ba toh gara ya kyaleta

dakin kakarta ta je ta gaisheta da sauran matan gidan sunata tsokanarta malam yaje biko kenan

lababawa tayi ta dauki kwalli cikin kayan kwalliyar dake cikin wani karamin kwando kafin tace

goggo habi ance anyi baki a gidan nan suna ina ?

suna can sashen malam dan basuji dadi ba kam dan gamo sukayi.

zaro idoo tayi gamo fa a ina?

can tsallaken lawoli dan sai dazu jibrin yaje ya dauko motar su ma dan can suka barta

oh Allah ya kiyaye gaba bari naje in gansu

toh maxa kam dan dare yafara yi kizo ki tafi gida in kuma nan kwana to

ah ah niba zan kwana a nan ba

oh dai ke kika sani

sai da ta tsaya lungun bangaren ta zazzana kwalli ta fito aljanar sakkafin ta nufi dakin datake jiyo maganar su da alama waya daya yakeyi daga cikinsu

cikin sanda ta qarasa qofar dakin cikin sa'a tana zuwa ana kawo wuta inda haske ya gauraye dakin baki daya kasancewar habeeb ya juya bayane yana shan fura da kyar da dabara sbd bakinsa shi kuma nasir yana waya hankalinsa be kawo inda take ba shiyasa basu ga tsayawaer ta ba

Angaishe ku fitinannun bil adama masu kunnen kashi....

TA ME GARI

na
khadija usman

5

cikin kwanaki kadan aka gamawa dije komai na makarantar ta arabi da boko kasancewar Alhaji khamis ba mazauni bane yasa dije ke fuskantar rashin jin dadin zama ga dukka mutanen gidan dan su nasir ba qaramar wahala suke bata ba saukinta daya bangaren masu aiki take shiyasa take dan samun rangwame duk tayi sanyi da dana sanin zuwa binni sam inbanda karatu ba abinda tamaida hankali akai

dawowarta kenan daga makaranta ta shiga tayi wanka dan dama bata son kazanta duk shakiyancinta man basira me aiki take shafawa duk da vaseline ne amma bawani duhu datayi koba komai cimar kauye da ta birni akwai banbanci kuma ga A.C dake ratsata daga school har gida dan makaranta me tsada aka sata kasancewar tayi primary daga nan inna tace bazata yadda taci gaba da karatun arna ba shiyasa ta hakura su kuma anan suka sata a J S S 3 bada jimawa ba jasu zana juinior waec kuma alhmdllh tana fahimta sosai ko yanzu data gama shafa mai niyya tayi tadanyi kwalliyarta amma data tuna in tayi anan za'a yi mata dariya hakan yasa tafasa yi tunda bata iya ta 'yan birni ba har yanzu dan kayan kwalliyarta tun na gida ne

fitowarta yayi dai dai da fitowar habeeb wanda ya zuwa yanzu yasa an mayar masa da hakorin roba a inda yasamu gibi baza'a taba ganewa ba tafiya yakeyi yana waya da alama hirar ta soyayya ce duba da yadda yaketa lumshe ido tare da karya murya

fitowa tayi zuwa kitchen dan tadau abincinta sanye take da riga da sicket na atamfa se yawo takeyi cikinsu kusa. dinkin kauye sam bata lura dashi ba har saida takawo kusa dashi kamshin hadadden turarensa na indunusia ya bugi hancinta wuceshi tayi ta shige tadauko abincin ta dai dai tazo fitowa sukayi karo miyar agushi ce da tuwon shinkafa duk ta hada a kwano daya hakan yasa malmalar tuwon tayi kasa yayin da miyar tasauka jikin farar T.Shirt din dake jikinsa ta gangara kasa aikuwa take ya saki wata 'yar qara sakamakon miyar nada dan zafi dan kun san manyan coolers na riqe zafi sosai

dan ja haya tayi kadan a dan tsorace dan sam bata bukatar wani abu ya hadata da wadan nan azzaluman dan haka kawai ma in sun so wahalar da ita sukeyi suyita cewa tayi musu kukan aljanu ko wani abun in takiyi su daketa bare kuma yanzu data tabbatar tayi laifi ai bata gama tunani ba taji saukar tagwayen marin dasai da kanta ya bugu da fredge din dake wurin wata qara tasaki wadda mamy ahigowarta kenan ita da naair da wata budurwa wadda bata santa ba nasir jaye da troly koda suka shigo suka ga meya faru iyakar kuluwa mamy ta kulu yayin da naseer ya fara bala'i yana qara fadin ya tsani yarinyar nan shiko habeeb tunda ya mareta huci kawai yakeyi yayin da yake qara jin tsanar yarinyar har cikin ransa

budurwar dake tsaye ce ta yamutsa fuska tare da fadin mamy pls where did u get dis poolish basterd girl?

hamm yusra she's from Alhaji's village !!amma gaskiya kinyi sake mamy dubi fa da abincin da zata cinye amma dai daddy yaqara yawan abincin gidan ko dan kin san mutanen qauye da ci basu san wani mentaining ba burinsu kawai ciki yadauka musamman tuwo basa masa wasa bare anga farin tuwo

tsaki habeeb yaja kafin yace ai zataci ubanta wlh yau bazata ci abinci a gidan nan ba

nasir ne yayi caraf da cewa iya yau kawai ai wlh sai jibi kafin taci

wlh ni kwana uku ma yakamata tayi dan ubanta intaji wuya dakanta zata koma kauye ai shegiya me siffar 'yan ruwa dariya duka suka sa banda habeeb da ya qara hambareta ya juya ya fice nan suka gama mata tujara kafin suka barta a gurin bayan mamy tasa basira ta kwashe tuwon daya zube ta kuma tabbatar kar abawa dije abincin dare

a gurin suka barta tanata kuka yayin da tayi me isarta data tuna innarta da baffanta can kuwa saita yi shuru ta furta a fili ina dalili zan zauna ana cutar dani yaseen bazan yadda ba gara in koma dijeta ta da dije masifa dije bala,i dije annoba jahannama ga fasinja uwar mazga bari inga wato kai kace yau bazanci abinci ba yau toh wlh kaine bazaka cishi ba har sai gobe kajawa kanka kai kuma uban 'yan mugunta kace bazanci ba har sai jibi toh kaima sai jibin kaci ku kuwa masu cewa sai nan da kwana uku toh kuwa sai lokacin zakuci dukanku dariya tayi ta mike tana taba inda ya mareta ta jinjina kai ta tashi ta shiga dakinta

kudin da daddy yabawata last week yace inta tashi siyen wani abun basaita tambaya ba dan haka ta boye su bata ma siye komai ba su ta je tadauko ta fito zuwa farfajiyar gidan

gurin bala driver ta nufa inda yana ganinta ya shiga washe baki

qarasawa tayi cikin sakin fuska ta duqa har kasa ta gaisheshi ya amsa cike da jin dadi kafi. tace dama aikoni akayi yace toh toh ya akayi?

gashi hajiya tace kasiyo mata maganin kashi

wane irin maganin kashi kuma?

eh wai bakuwar nan ce dasuka zo tare yau kwananta goma batayi kashi ba shine tace a siyo mata wanda zaisa tayi sannan wai da maganin na wanda in an yaye yaro ake bashi dan yayi bacci wai yaye za'a kawo mata yau shine tace a siyo mata shi

toh kaao kudin amma ina su Alhaji karami ai su suke shigo da magani gidan in ana buqata

wai mantawa sukayi shiyasa tace yasiyo sachet goma sha biyu biyu dan a ajiye sbd gaba

toh yafada tare da miqewa ya tafi dan akwai wani pharmacy nan bayan layin

guri tasamu tazauna dan ta jirashi har ya dawo

hhhhhhhh mudai je zuwa

TA ME GARI NA khadija usman

gaskiya naga soyayya yau Alhmdllh naga sakonninku masoya wannan buk din banyi niyyar posting yau ba amma gashi nayi muku kyauta sadaukarwa ga dukkan masoya dijangala ta me gari

3

wata irin bugawa kirjinsu yayi a tare inda nasir ya bude baki da niyyar yin ihu tace kanamin ihu bakinka zai tsaya a haka har abada gum yayi banda zufa ba abinda ke ketowa ita ko se raba ido takeyi a dole aljana habeeb dake zaune bakinsa fal da fura dan yakasa hadiyewa karasawa tayi cikin dakin yayin da dukansu yau saida sukayi fitsari dariya ce fal cikin dije amma takasa yi ta gintse kallon kwaryar gaban habeeb tayi taganta cike da fura tab wadda duk iya shansu basu isa su shanye ta ba bare ma taga 'yan binni kadan suke cin abinci ko a film in an nuno hmmm tace a zuciyarta ta furta yau zakusha azabatul ula kallon su tayi taga yadda suke makyarkyata tace wato bakwajin magana ko ? ko a cikin bil'adaman naga ku takadirai ne kun takamin yara sunacan sun sami gocewar kashi a tsakiyar kansu  amma ku kuna nan kuna shan fura ba ruwanku ko sannan danace kada ku dauki abin hawanku sai gobe shine kuka tura jibirila dan me gari ya dauko ko sbd kun raina izayar jinni toh tunda yarana suna halin jinya yanzu kuma bari in kwantar daku dan mai maganinsu ya fadamin yace sai sunyi shekara dari uku da saba'in kafin su warke abin takaicin ma gasu 'yan biyu ne ko yayesu banyi ba duk jarirai ne basu wuce shekara dari da ashirin ba gashi kunja musu jinya tun suna rarrafe dan haka tunda kuma ku biyu ne yanzu zan yi muku abinda kukayi musu kashin tsakiyar kanku zan malkwadar yadda zakuyi jinya tare

wayyo Allah nadan girman Allah kiyi haquri wlh wlh bamu san da yaranki a gurinba dan ya rasulillahi manzon Allah sallallahu alaihi wasallam dan binta 'yar ma'aikin Allah nanfa suka shiga rokarta duk da dai shi nasiri a iya bincikensa besan da wani kashi a tsakiyar kai ba amma ba mamaki a halittar aljanu akwai shi su kuma ta tsinka musu jijiyar kai yau sun shiga uku shi wlh da yasan haka ne wlh da be zo kauyen nan ba shiyasa mamy bata son su zo a fannin habeeb ma haka kukan zuci yakeyi yayin daya saki baki furar ta zubo dan iya tashin hankali yana ciki a rayuwarsa ba abinda ya ke tsoro irin aljani yau saiga shi garin tukin ganganci irin na naseer yaje ya tsokano musu su kunji fa sharri readers

katse musu tunani tayi ta hanyar ce musu zanyi muku afuwa amma da sharadi

da sauri sukace mun amince wlh ko meye mun yadda mudai ki dena zuwa mana

toh in kun yadda zaku shanye furar nan duka yanzu

zaro ido sukayi waje tare da fashewa da kuka musamman nasir da a duniya ba abinda ya tsana irin fura

cikin marairai ce fuska da kuka ya hada hannunsa biyu yace dan girman Allah kiyi hakuri wlh bana shsn fura danasha amai zanyi ke zan iya kwanciya ciwo ma

oh to to tunda baka shan fura bari a sake maka hukunci zan daure cikinka kadaina kashi da fitsari tsawon shekara goma zan kanne maka ido daya zan toshe maka kofar hanci daya da rabin bakinka zan......

ya isa dan Allah kiyi hakuri wlh zan sha kafin tayi wata magana tuni sun fara shan furar inda suka dinga kokawa da ludayi a cewarta basa sha sosai zata kawo musu irin tasu ta aljanu aikuwa suka bada himma sosai inda suketa sha cikinsu ya cika dam gashi furar ko rabi batayi ba dan su a ganinsu ma kamar qarata akeyi bata ankara ba kawai taga sun fashe da kuka a tare abinda yabata dariya kenan wai babba da kuka abinda bata taba gani ba sai a talabijin dan haka batasan lokacin data kama dariya ba su suna kuka ita tana dariya gashi dai furar nan shanta suke

motsi taji alamar za'a shigo gurin ganin sun duka suna kallon fura suna kuka yasata saurin barin gurin ta labe bayan dakin dan wani lungu ta fara dirje bakin fuskarta

da sallama malam ya shigo gurin turus yayi ganin su sai gunjin kuka sukeyi suna shan fura

subahanallah ya fada yana me kiran sunan su jin muryar malam yasasu dagowa suna fadin yauwa malam aljana wlh tana dakin nan sun rude gaba daya yayin da itako tana jin suna aljana ta dira ta katanga tayi dakin kakarta tana fadin ni nayi gida dan nama fasa zuwa gaida bakin saida safe nazo

au da duk kina ina ja'irar yarinya nama aza kinyi gida

toh ban tafi ba sai yanzu nayi niyya ehee

mificin hannunta tajefo mata ta kauce tana dariya ta fice daga gidan

sosai naseer ke amai ya galabaita matuka inda hankalin malam yatashi sosai dan shima habeeb zazzabi ya rufeshi ba shiri malam yasa aka dauko mota aka nufi asibitin cikin gari dasu dan basu taimako dan shi lamarin yana bashi mamaki wai aljana kuma duka su biyu ke ganinta saida aka sa musu drip dukansu aka musu allurai kafin suka yi bacci amma a dan wannan lokacin duk sun rame

********

tunda abin nan yafaru bata qara zuwa gidan malam megari ba dan ita tama manta da wasu baki yau kusan kwana hudu kenan tadai ga innarta na yawan zuwa gidan me gari

yau da wuri ta tashi ta share gidan tsaf duk da shekararta sha hudu yanzu amma tana aiki sosai sai dai in bata so ba yau dinma dan tanason ta bi su sadiya cikin gari dan zasuje gidan yayar sadiyar ne dan haka takevtaya inna aiki dan karta hanata

****
a gajiye suke likis sbd tafiyar kasa da suka sha dan haka tasamu gefen hanya ta zauna tana mayar da numfashi kamar wadda tayi gudu cikin tsananin gajiya ta dubi sadiya tace yaseen bazan iya qarasawa gida a kafa ba wannan ai sai in mutu kafin inkai

to ai laifinki ne dije an bamu darinmu ta ihemu mu hau mahin kika tahi kikace a rabeta kowa ya kahe nahi to gahinan ai sawun mu ya fada mana dan ni wlh ji nakeyi kamar ba a jikina kafafuna suke ba

toh ni uwarku ce da in nace kuyi abu he kunyi a wane dalili toh wlh duk wadda taqaramin harri banyi abu ba tace nayi hena mazgeta hegu kawai
.gum sukayi sun san sauran dan duk wadda tace kala yanzu uwar mazga zata kaddamar musu

kunga ku tahi mu tare me mahin ya kaimu gida

to ina kudin ? cewar shatu

ku zo kuji dabarar dana shirya duk suka hada ka wunansu guri daya kome suka ce oho naga dai sun rushe da dariya sannan suka mike suka fara tarar dan mashin
sun tari mashin yakai goma ba wanda ya tsaya sai daga baya wani saurayi ya tsaya yace ina zaku ne 'yammata?

nan Gawo nawa?

toh ku bada nera sittin tunda ku uku ne

ah ah malam cewar dije uku hamsin in yayi maka

dariya abin yabashi wai uku hamsin dan haka yace to ku hau nan suka dane mashin dukansu sannu har suka iso cikin gawo dai dai gidan me gari inda dan wani tudu yake suka ce masa ya isa ya tsaya yanata zuba musu surutu sukuwa wannan ta kalli wannan ta kalli wannan da haka kuwa sai yaga hafsi da shatu  sun kwasa a guje dije ta yunkura yayi caraf ya riketa aikuwa dan da nan kallo yadawo garesu inda yara suka fara taruwa harda 'yan manya manya kan kace me guri ya cika dam tuni lbr ya isko gidan megari yana zaune dasu habeeb dake shirin komawa gida gobe dan Alhmdllh sun sami sauki dan megari yayita amso musu taimako maganin iska kuwa da tsari duk anyi musu shi suna zaune suna tattaunawa akan gidajen da basu je ba yau zuwa gobe zasu je na kusa kusa na nesa kuma sai sun kuma dawowa ana haka aka zo aka fadawa me gari wai ga dije can tayi sata an kamata cikin sauri ya mike duk da jikin tsufa amma kalmar tayi muni sata!!!sata fa toh meta sata ?

ganin yadda maganar ta shigeshi yasa su habeeb tambayar sa wacece dije?

kanwarku ce diyar gurin inusa

ku tashi muje duka suka miki suka bi shi

koda suka iso gurin sun iske dandazon mutane an taru koda akaga me gari kowa ya ratse yabashi hanya ya isa gurin inda yaga dije tsaye me mashin ya rike mata hijabi itako ko a jikinta tanata gwagwiyar goruba

rasa ma me zai ce yayi inda ya qarasa yana fadin malam dan Allah sakarta mana

wlh baba bazan saketa ba sai an biyani kudina

nawa ne kudin naka?

naira hamsin ne

yanzu kai da duk akan nera hamsin katarawa mutane wannan jama'ar

toh ai hakkina ne naga kuma akan sana'ata ne

toh garin yaya kudi ya hadaku?

nan yakwashe komai yafada masa aljihu ya laluba ya ciro nera dari yabashi yace yabar canjin sannan yasaki dije malam yakama hannunta suka nufi cikin gida su habeeb sam basu lura ba dan suna waya ne da mumy sai da suka gama suka juya suka hango bayan me gari rike da hannun wata yarinya ze shiga gida nan suka nufi gidan suma

tsaye ya tadda matansa da sauran ahlin gidan duk tsaitsaiye suna jimamin abin nan yabasu labarin ainihin abinda yafaru kowa ya kalli dije wadda har yanzu bata cewa kowa kanzil ba tanata dai cin goribarta ana haka su naseer suka shigo kasancewar dije ta juya baya nan suka tambayu meya faru nan malam ya shiga sanar dasu cikin zolaya habeeb yace tab ashe kuwa yau sai na bawa budurwar kauye kashi dai dai nan dije ta juyo akayi ko sa'a tasha kwalliyar nan sai dai yau jambaki tasaka kanta kile sabanin baya

wani uban ihu naseer yasaki inda shima habeeb ya karba suka fara fadin gata nan itace suka kwasa da gudu sai dakin inna dudu suka rufo

mamaki ne yakama kowa yayin da dije ta zube a gurin tanata dariya ganin haka malam ya dauka shedananta ne dan haka be bi ta kanta ba ya nufi dakin da suka rufe anyi anyi su bude sunki dije ce ta taso tazo dai dai kofar windo ta leka tace in baku bude kofar nan ba saina kwakule muku idanu da sauri suka taso suka hau kokawar bude kofa tun daga nan malam ya fahimci karatun suna budewa dije ta kara fashewa da dariya zasuyi ihu me gari ya buga musu tsawa yace dama wannan ce aljanar datake tsorata ku?

eh itace wlh itace shi kanshi me garin yaso yin dariya ganin yadda duk jikinsu ke kyarma

to ai itace kanwarku diyar babanku inusa a shakiyancin dije nasan zata aikata fiye da haka

dimmm sukayi gaba dayansu inda suka kai dubansu ga dije wadda ta dallaro harshe tare da yimusu gwalo tace ni ba aljanah bace gyadata kuka takemin ta zube ina shirin in tsince naji fitsari na juya inyi koda na juyo naga kun takemin ita shine nayi maganinku

tunda tafara magana zuciyar mazan tahau lugude musamman. habeeb da yayi asarar hakorinsa guda na kasa saboda abin wayyo Allah.

KARANTA: Zafin Kai Hausa Novel Complete By Mamuhgee

muje zuwa readers yawan comments yawan page

na
khadija usman

6

wannan shafin sadaukarwa ne ga dukkan member's na khadija fans novels hakika naga ruwan comments da kuma masu bina pc nagode sosai Allah yabar kauna*

       ta jima zaune kafin daga baya taji alamun dawowarshi mika mata yayi tare da canjin tace ya rike canjin ta karbi maganin a bakar leda ta shiga cikin gidan

tunani ta shiga yi shin wai ta inama zata fara ne wai wazata fara yiwa illa habeeb,nasir,mamy,ko uwar mugaye yusra ah ah takan ya habeeb zan fara tunda shi yafara min mugunta

mikewa tayi ta shiga kitchen cikin sa'a ta riski basira na zuba coffee cikin cups kallonta tayi tace sannu da aiki Anty na

murmushi basira tayi yayin data kamo hannun ta cike da tausayawar abinda aka mata dazu tace sannu dije kiyi haquri da abinda ke faruwa gidan nan ki dinga taka tsantsan da hajiya dan wlh batada imani suna iya hanaki abincin kwana ukun dasuka ce dan haka kada kidamu zan dinga boye miki a daki da zarar kin tashi ci zan nuna miki inda zan dinga ajiye miki

dariya dije tayi kafin tace kada ki damu Anty ai daga yau har zuwa kwanakin da suka dibar min zanci abinda raina ke so ke dai kawai kisa ido kiyi kallo nice fa dije wlh a kauyenmu anno ba ake cemin duk gidan dana leqa saina sasu jinya dan haka sai sun san nice sukawa haka da naso in canza amma naga basu san kara ba gara ayi gwari gwari

mamaki ne yakama basira inda take kallon dije daketa zaro zance ba wakafi ba aya duk da take qaramar yarinya dan ita a ganinta bazata wuce shekara sha biyar ba amma ta iya tsara zance kamar redio amma kuma in akayi la'akari da dabara irin ta mutanen kauye wannan ba komai bane

farantin data dora kofunan akai ta dauka da niyyar fita dije tace ina zaki kuma Aunty ?

wadan can 'yan sudan din zan kaiwa shayi wai da yamman nan kin san su

ah ah kawo inkai musu ki huta ai kinyi aiki kin gaji naga ma kamar bacci kikeji dan haka  jeki kwanta ki dan huta zan qarasa  aikin kije ki

toh kadafa kije suyi miki wata muguntar kuma

ah ah ba komai ai haquri zan basu kada ki damu

mika mata tray din tayi ta fita dai dai wani dan corridor ta labe ta fito da ledar daga jikinta ta bude juya maganin tayita yi dan ta rasa na bacci dana kashi kawai shahada tayi ta babbala sachet daya a cikin biyun ta juye cikin daya kofin dayan na hannunta ta fara barewa shima da alama kam wannan shine na baccin tafada a bayanne dan naga shi inna ta siyawa Ahmadu lokacin data daukoshi yaye shima duka guda goma ta juye ta dinga juyawa har duka suka narke kafin ta mike ta boye sauran a wani loko inta dawo ta dauka ta nufi part dinsu

ta dan jima a tsaye kafin daga haya tayi knoking

shigo  kawai basira taji ance murda handle din kofar tayi ta kunna kai parlon da sallamar ta habeeb zaune daga shi sai boxer da singlet yana zaune yana duba system dinshi da alama wani aikin yakeyi me muhimmanci duba da yadda yamaida hankalinshi gaha daya ga abinda ke gabanshi

shiko naseer jallabiya ce a jikinshi yana zaune yana danna waya da alama charting yakeyi

naseer ne ya amsa sallamarta inda ya dago idonsa tare da wurga mata harara uban me yakawoki dakin nan ?

um dama itace batajin dadi shine tace in taimaka in kawo muku

tsaki yaja kafin ya maida hankali ga wayarshi

qarasawa tayi ta durkusa ta ajiye cup daya a gabanshi sannan ta nufi gurin habeeb shima ta ajiye masa nashi shi kam ko kallonta beyi ba dan haka ta mike ta nufi hanyar fita

har takai kofa taji muryarsa yana fadin idan naqara ganinki a dakin nan wlh saina lahira yafiki jin dadi shegiya me siffar aljanu nunar rana kawai

itadai bude kofar tayi tay ficewarta inda shi kuma ya jawo coffee dinsa yafara sha jiyayi na yau yafi na kullum dadi dan wani kamshi da dan zaki zaki yayi dan haka ya dinga sirba baji ba gani shima naseer haka yayita sheqe abinshi inda shi kuma beji wani canji ba

hamma yake tayi baji ba gani yayin da  yafara ganin uku uku dan haka ya mike ya nufi bedroom yana tangadi kamar dan maye sam yarasa wannan wane irin bacci ne yazo mai lokaci daya

naseer daya bishi da kallo yana ambatar lfy dai bros naganka ka sauya

cikin murya irin ta wanda bacci yakama sosai yace lfy qalau kawai bacci nakeji bari in dan matse duk da naga yamma tayi

ok a tashi lfy

bai bashi amsa ba ya shige ciki kawai shi ko yaci gaba da abinda yakeyi

yana cikin haka kusan minti talatin yaji cikinsa yayi wata irin murdawa da ya dan share amma daga baya yaji bazai iya ba dan kamar ba haya yakeji dan haka ya mike ya shiga toilet din dake falon yana ko shiga yafara antayo abinsa rai fesss

itako dije tana fita kicin ta koma ta tarar da basira harta koma daki freidge ta bude ta fara kwashe lemukan ciki kamar wadda aka sa guda biyu kawai ta bari ta dauko su ta bude tare da zuzzuba wannan maganin kashin aciki kowanne sachet daya daya kana ta mayar ta rufe alamar motsin tafiya taji cikin sauri ta rufe friedge din ta tashi ta nufi cabinet tajawo filet ta kama daurayewa kamar me wanke wanke

mamy  ce ta shigo kitchen din tana kiran sunan basira ganin dije a tsaye tana aiki yasata tambayar ina basira ta shiga?
batajin dadi ne shine nake tayata kanta ke ciwo ta sha magani ta kwanta

wani wawan kallo mami ta watsa mata kafin tace hmmm ai dama aikin shiyafi dacewa dake a gidan nan maza ki daukomin lemo a friedge ki kawo mana dinning muna jira zamuci abinci

toh ta amsa ita kuma mamy ta juya ta fita

dariya dije ta fara yi tare da fadin komai kuke so zanyi muku amma ni da lfyr ku zan fanshe

lemukan ta diba ta nufi falon inda ta iske mamy da yusra har sun fara cin abincin ajiye lemon tayi da niyyar juyawa taji yusrah tace

ke aljana me siffar tumatur uban waye zai zuba miki lemon toh

dawowa tayi ta bude ta zubawa kowa ita gwara ma da suka ce ta zuba musu din dan da sun taba murfin da da kansu zasu gane an bude lemo a zuciyarta tana jinjina kalar muguntar da zata yiwa yusrah dan da Alama tata saita fi ta kowa barin gurin tayi da sauri ta nufi dakinsu

inda su hajiya aka baje koma aka dankari abinci da drinks. kasancewar lemon da sanyi kuma na roba ne shiyasa suka kusa shanye su dan kadan suka bari

sun dan jima suna hira kafin mamy taji cikinta ya murda alamar tanajin bayan gida

mikewa tayi ta shiga bedroom dinta ta afka toilet

ita ko yusra ta dan jima kafin itama taji yanayin na hajiyar itama ta mike ta shige dakin inda ta afka toilet tafara zabga nata tutun

*******
shi kam naseer abin ba'a magana domin kuwa ya zuwa yanzu ya tabbatar cikinsa yadan rikice dan haka ya dinga zarya zuwa toilet abun mashi har bashi tsoro yakeyi duba da yadda yaketa zaryar toilet ga muntar sa harya fara zafi

bangaren habeeb kuwa baccinsa yakeyi kamar wani matacce

bangaren su hajiya kuwa abin fa ya ci tura inda suketa zaryar zuwa toilet ganin abin yana neman wuce gona da iri yasata lalubar wayar habeeb dan ya zo yakawo mata magani ta kira yakai sau biyar be daga ba hakan yasa ta kira number naseer shima din shuru domin yana toilet ya na ta zabga abin tana kokarin kara kira yusra ta shigo dafe da cikinta tana dukawa mamy na bude baki da niyyar tambayarta taga ta kwasa da gudu tayi toilet din dakin itama cikinta sake murdawa  yayi inda ta tashi da niyyar shiga toilet din taji shi gam a bame koda ta dan yunkura tana rawar disko irin ta wanda kashi inya matsi mutum taji kawai ya zubo mata

ku biyoni


TA ME GARI

NA
khadija usman

7

     wayyo Allah cikina mamy ta fada tare da dukan kofar toilet din cike da maseefa takama fadin wai ke yusra uwar me kikeyi a bandaki har yanzu ko kashin danko ne ai ya ci ace kin gama to waima ina na dakin da kike shine sai kin taho nan

a wahalce yusrah ta bude kofar toilet din kafin daga bisani tasa hannunta ta toshe hancinta kafin tace mamy wlh gudawa nakeyi dazu kam da dan dama dama amma yanzu kamar ruwa nake yinta ni tsoro ma nakeji kar inje ko amai da gudawa zanyi

cikin mamy ne yayi wata qara bata san lokacin data buge yusrah ba ta afka toilet itako yusrah bin wajen da mamy ta tsaya tayi da kallo tare da fadin mamy kema gudawar kk yi ashe?

******

kwance take kan katifa amma tunaninta nacan gurin masu zawon gidan dan haka ta mike ta fita zuwa falon akan idonta yusra ta fito tana tfy a dudduke kuma a botsare ta kuma dafe ciki kallonta dije tayi kafin tace sannu anty

harara ta wurga mata tare da fadin dan uwarki ciwo kikaga inayi da zaki cemin sannu

kuri tayi da ido takama dariya kasa kasa sannan tace ah ah dana ganki haka ne saina ga kinyi kama da masu ciwon zawo amma kiyi haquri tsaki tayi kafin taja qafa ta bar gurin inda dije na ganin ta shige ta kife a gurin tana dariya saida tayi me isarta kafin ta mike ta nufi kitchen tana shiga ta bude drower ta fito da bucket din da ake zuba kaji idan an soya ta zauna zaman dirshin tare da dauko lemo jin alamun ya huce ba sanyi yasata tunawa da ita ta kwashe su dazu ashe tsaki tayi ta mike ta nufi friedge din falo ta dauko exotic me sanyi ta zauna ta fara yagar naman tana shan lemo kuma saida taji kamar cikinta ze fashe kafin ta mike da kyar tana hamdala har tazo fita a kicin din ko me ta tuna kuma oho? sai naga ta juyo ta shiga store ruwa ta dauko carton daya ta nufi friedge dasu duka ta bude ta dura maganin nan a cikin kowacce gorar ruwa kafin ta jera su a friedge dan tasan suna cikin wannan halin bazasu buqaci lemo ba sai dai ruwa saida ta gama shirya su ta miqe tabar kitchen din takoma daki

******

sam yakasa gane meya rikita cikinsa haka lokaci daya dan ya zuwa yanzu yayi bayan gida sau ba adadi dan haka da himma ya qarasa inda wayarsa take ya dauka danya kira docter yusif abokinsa yakawo mishi magani ganin missed calls din mamy yasashi fara kiranta amma bata daga ba yasan bazai wuce zancen aiken datace zatayi masa ba shi kuwa a wannan yanayin dayake ciki ba inda zai iya zuwa dan haka jin bata dauka ba yasa shi kuma be sake kira ba dan haka ya kira doctor yusif yana dagawa yasanar dashi abinda zai kawo masa ya kashe wayar

minti talatin sannan doctor yusif ya iso direct part dinsu ya nufa yana zuwa lokacin naseer yana fitowa kenan daga toilet yana ganinshi ya mika masa hannu pls bani maganin nan kada in mutu dariya yusif yayi kafin yace lallai abin nan yadameka sosai so gashi ko karba yayi kafin yace pls dan bani ruwa a friedge din nan

yana dubawa yace ba ruwa sai lemo

kai pls kaje cikin gida ka daukomin pls

fita yayi yaje kitchen yadauko yana fitowa yaga mamy ta fito ta nufi dakin da yusra take

mamy ina yini?

juyowa tayi ganin yusif a tsaye yasata hamdala tare da fadin lfy qalau ya aiki ?

lfy qalau alhmdllh

abokinka kuwa yana nan dan nakira wayasu duka basu dauka ba

eh yana nan bejin dadi ne wai

subahanallah meke damunsa ?

wlh wai zawo yakeyi yanzu haka wani abun yaci kin sanshi sarkin ciye ciye a waje

sai yanzu tayi tunanin irin cimakar dasuka ta ci kuma duk laifin yusra ne ita tasa sai an siyo gashi nan taja musu shegiya gashi yanzu taja musu rudewar ciki

jin cikinta ya dan juya yasata fadin am kanaji yusif inka shiga wajen nasa ka kawowa yusra maganin itama tasha dan itama cikinta ya dan birkice

ok mamy ya fada tare da juyawa ya nufi hanyar fita

ka danyi sauri dan Allah

insha Allah yanzu zan dawo

be wani jima ba sai gashi yadawo aikuw a da sauri mamy ta nufi kitchen tadauko  gorar ruwa tun a can ta bude maganin tasha dasauri ta nufi dakin yusrah ta bata itama tasha

********
toh fa abu kamar wasa gida ya kacame da 'yan zawo abincin da basira tayi ba wanda ya kalleshi se dije da duk abinda su mamy ke ciki ta sani hankalinta kwance ta zage ta dirki abincinta

******

washe gari sai wajen qarfe goma yatashi da kyar ya iya bude idonsa domin nauyin dasukai masa  jikinsa yakeji wani iri duk ba kwari haka ya lallaba ya tashi ya shiga toilet dan yayi wanka yayi sallar magrib wanda shi a tunanisa bai jima yana baccin ba

ganin toilet din kaca kaca yasa ranshi ya baci shin wane dan iskan ne yayi haka da wurin yana cikin haka yaji an turo qofar da qarfi koda ya duba naseer ne baiko bi ta kanshi ba ya sabule wando ya fara nishi harda 'yan hawaye domin yazuwa yanzu gudawar ma taki zuwa sai majina toh inama yaci abincin dazai narke yazama kashi tun jiya yake yin abu daya ina yaga lokacin zaman cin abinci gara ma ruwa danshi yana sha sosai maganin da yusuf ya kawo masa kuwa duk ya shanye su amma a banza ga mamy ma ya kirata tace mishi itama hakan take amma tasan be rasa nasaba da ciye ciyen da yusra tasa sukai tayi tsakanin jiya da yau ya tsinewa yusra tare da ja mata Allah ya isa yafi sau nawa

zuba masa ido habeeb yayi ganin yadda yaketa faman nishi harda 'yar kwalla ga uwar zufa dayakeyi kuma inba abin ya girmama ba yasan ba yadda za'ayi naseer ya iya irin wannan lalurar a gabansa dan haka hankalinsa tashe ya nufi gurinsa yana fadin sannu bros meke damunka haka?

nishi yayi kafin yabashi. labarin cimar da sukayi jiya inda ya fada mishi su mamy ma nacan na fama

subahanallahi ai ban sani ba meyasa baku fadamin ba

duk da halin dayake ciki saida ya fella masa harara kafin yace ta ina za'a sanar dakai ka kwanta bacci kamar gawa kasan ko tashi nawa nayi maka amma bakaji ba

ya Allah wlh ni kaina ban san wane irin bacci nayi ba me nauyi haka yanzu haka wlh be isheni ba

kaga malam nidai dan girman Allah taimaka kasamin drip kar ruwan jikina su ida qarewa jini ya biyo baya

toh ai abari dai inyi wanka in rama sallolin da ake bina ko

toh yi maza kayi naseer yafada tare da mikewa yayi tsarki ya fita yana dafa bango

******

hankalin habeeb ba qaramin tashi yayi ba domin kuwa gidan duk na 'yan gudawa ne dole ya kwashe su duka ya nufi hospital dinsu dasu domin dole asa musu drip da sauran allurai wannan kashi sai kace annoba

itako dije komai akeyi akan idonta inda taketa dariya basira ta kalleta tace ke wai lafiyarki kuwa?

wlh qalau nake kawai murna nakeyi ina cikin farin ciki su da sun dauka in ta zama suna dimata kamar jaka ina kallonsu wlh kadanma suka gani daga yanzu duk wanda ya qara yimun wani abu na mugunta saina sa shi rawar nanaye

kallonta baseera tayi cike da mamakin maganar ta tace kina nufin kece silar rashin lafiyar 'yan gidan nan?

sosai ma kuwa Aunty ai baki sani ba ma wlh kadan suka gani tunda suka sa nadawo dijeta ta ainihi

kallonta kawai basira takeyi tare da yaba qoqari da muguntar yarinyar dole itama tayi hankali da ita dan kar wataran tasata rawar nanayen itama

miqewa dije tayi ta tafi ta bude friedge ganin babu sauran ruwa ko guda daya yasata qara fashewa da dariya harda kwalla kafin tace sai ni dije uwar mazga ba'a min ba ma nayi bare anyimin

*****


kwanan su mamy biyu a asibiti duk sun rame inda gudawar ta tsaya cikin ikon Allah

yusracan dada ramewa hakora sun bayyana daddy dake  zaune gefen gadon da mamy ke kwance yana ta fadan meyasa suka ci abinda sukaci waje wasu basa inganta tsaftar kayansu gashi nan sun jama kansu ai nan yagama me isar shi kafin daga baya ya shiga dawai niyar kula dasu

kwanansu biyu a asibiti ana musu karin ruwa kafin aka sallamosu zuwa gida

koda basira ta gabatar musu da abinci cewa sukayi basa ci kayan fruit kawai suka dinga sha dan sunyi losing Apetti basu jin dadin komai

itako dije rai fesss domin makarantart ake tafiya hankali kwance

yauma shigowarta kenan ta hange su mugaye a zaune cikin garden su uku sanye take cikin unifoam dinta riga da wando da farin hijab qarami

tana shirin shigewa taji muryar naseer na fadin

ke Aljana dan ubanki baki iya gaisuwa bane ?

qarasawa tayi inda suke daya bayan daya ta gaishesu ba wanda ya amsa sai baqon da suke tare dashi

mikewa tayi da niyyar tfy naseer yajawota ya zuba mata rankwashi aka sai da ta danyi kara bata san sanda ta furta kaci bashi a fili ba......

mu kara wuta
ku biyo ni

*vote*
*comment*


4

dole in faranta muku masoyan ta me gari

jinjina agareku da godiya me tarin yawa masoya na kamar


jikin habeeb har rawa yakeyi sbd tsananin bacin rai haka ma ga Naseer sunma rasa me zasu ce ganin yanayin da suke ciki yasa me gari rike hannunsu tare da cewa dije ta tafi gida aikuwa ko kafin ta fita saida ta qara musu gwalo kowanne a cikinsu ji yakeyi idan ya riketa zai iya shaketa har saita mutu

malam ne ya shiga tausarsu da naseeha da nuna musu halin kuruciya ne

dan kawai tanada kuruciya sai akace tayi wa mutane halin dabbobi cewar naseer

kallonsa habeeb yayi kafin yace ai wannan yama wuce halin dabbobi ai sai na jakuna da tumaki irin na kauyen nan ma

sosai ran me gari ya sosu ganin yadda kiri kiri suketa zagin dije bama hakan yafi bata mishi rai ba irin yadda yaketa tausar su amma suna ta nuna kiyayyar su gareta inda har suke fadin baxasu je gidan su ba sam kenan hakan na nufin zasu tsiro da lalacewar zumuncin gidansa hmmm lallai dole yasan abinyi dan haka baxata taba sabuwa ba tashi yayi ya barsu anan sunata mita suka fasa fitar ma ko ina

*****

kwana megari yayi yana saqa da warwara kafin daga baya ya cimma matsaya tunda asuba a masallaci da suka hadu da yaransa da jikoki gurin yun sallah ya tsayar da malam inusa yace yana son magana dashi cike da ladabi ya amsa ya tsugunna gyaran murya yayi kafin yace kasamu labarin abinda yafaru tsakanin yaran nan nawajen khamisu da dije?

eh nasamu lbr gurin su ayuba jiya da dare har na bata kashi ma sosai

toh Alhmdllh amma banso ka daketa ba sai dai nagama yanke wani hukunci wanda ban sani ba ko zai yimaku dadi a matsayinku na iyayen khadija

insha Allahu baba duk abinda ka yanke nasan me kyau ne bazai cutar damu ba

masha Allah Allah yayi maka albarka

Ameen

dama bawani hukunci na yanke ba illa na turata birni can gidan shi kamisu din inyaso tasamu ilimin zamani itama sannan su fahimci junansu da zumunci me karko dan iya jiya da suka san juna naga alamar gurbin kiyayya a idon yaran sbd kuruciya shiyasa nake son ta zauna gidansu nasan zata samu rayuwa me kyau kuma zata nutsu domin inka duba kiriniya irin ta dije abin se addu'a

jimm yayi kafin ya nisa yace toh baba malam badamuwa Allah yasa haka yafi alkhairi sai dai mahaifiyar ita dijen sbd kasan gidansu sun tashi da akidar kin karatun boko shiyasa ko yanzu ta hana dijen tayi

kada ka damu inka koma kace ina nemanta zanyi mata bayani da kaina insha Allah nasan zata fahimceni dan tanada saukin hali

hakane nan yayiwa mahaifinsa sallama ya nufi gidan zuciyarsa cike da damuwa dan yana son dije kuma gashi a halin dije kauye ma ya aka kare bare binni kawai ba yadda zaiyi ne akan umarnin mahaifinsu

ba karamin fama malam yasha ba kafin inna saudi ta fahimceshi inda daga baya ya yi mata nasiha nan ya fada mata yau zasu tafi dan harda shi

koda aka fadawa dije abin mamaki murna ta dinga yi dan tana son rayuwar binni da kuma karatun boko dan haka ta shiga hada kayanta inda innarta ta dinga kallonta zuciyarta na tunanin inda 'yarta zata rayu gidan hajiya zahida macen dake kyamar mutane ko zuwa sukayi saita nuna a fili daga baya ma tace ta daina zuwa kuma kamar abin magani duk abinda ta ce ya zauna a gun Alhaji khamis

'yan tafiya sun shirya tsaf yayin da ba wanda yasan da tafiyar dije har saida aka zo tfy sannan akaga da malam za'aje kowa yayi mamaki zuciyar su habeeb kamar ta buga akan dole suka yi shuru dije ta shige mota ita da malam akaita daga musu hannu inda kawayenta keta murna da kuma kewar uwar mazga yayin da dayawan mutane ke murnar ala raka taki gona

*DIJE A BIRNI*

tunda suka shigo garin abuja ta zuro kai ta glass tana leke kamar zata fado yayin da malam keta murmushi yana tsokanarta ita kota kansa bata bi ba kallonta kawai takeyi sukuwa mazaje bakin ciki kamar ya kashe su da gayya nasir ya qara daga glass ai kuwa saida dije tayi kara dasauri malam yace lfy ?

bakomai baba malam bari zan rama

zaki rama me?

kai dai ka bari kawai kasan bana cin bashi ba'acin nawa dole in anci nawa sai an biya

toh Allah ya kyauta

Ameen

sun karaso gidan Alhaji khamis aljannar duniya inda cikin sa'a suka riskeshi kuwa ba karamin farin ciki yayi ba ganin dan tsohonshi a gidanshi kasancewar matar gidan ta fita shiyasa basu sameta ba nan bada bata lokaci ba me gari ya sanar da dansa komai da dalilin kawo dije kwarai ya nuna jin dadinsa inda nan take me gari ya nuna baxai kwana bazai koma dole aka sa drivrr ya mayar dashi ranar

******* me aikin gidan Alhaji ya kira ya ce tasa dije tayi wanka sannan ta bata abinci kafin hajiya ta dawo

koda hajiya ta dawo ba karamar rigima aka kwasa ba dan saida Alhaji yayi mata jan ido kafin ta yadda da zaman dije a gidan

KARANTA: Gidan Sarauta Complete Hausa Novel